Labarai
An Raba Kayan Agaji Tare da Sake Fasalin Albashin Dagattai a Kauru
Majalisar Karamar Hukumar Kauru dake Jihar Kaduna ta raba kashi na 2 na kayayyakin tallafin abinci da suka kunshi buhunan masara da shinkafa 600 kowannensu, a kokarin da gwamnati ke yi na rage wahalhalun da jama’a ke fama da shi sakamakon cire tallafin mai.
Da yake mika ragamar rabon kayayyakin ga Shugabannin kwamitin, wadanda sune zababbun gundumomi 11, Shugaban Karamar Hukumar, Alh Bashir Tanko Dawaki, Ya umurcesu su yi adalci kana su tabbatar kayayyakin sun isa ga mabukata da Marayu da masu lalurar nakasa da gajiyayyun dake gundumomin.
Alh Bashir Dawaki ya yabawa Gwamna Uba Sani na tallafin abincin da nufin rage wahalhalun da talakawan yankin ke fuskanta.
Da yake tsokaci a madadin shugabannin kwamitin wadanda suka karbi tallafin gundumomin su, kakakin majalisar kansilolin, Alh Hamisu Umar ya nuna farin cikinsa ga gwamnatin jihar bisa wannan yunkuri, ya sha alwashin zasu raba kayayyakin yadda ya dace
A wata sabuwa kuma, shugaban Karamar Hukumar Alh Bashir Dawaki, Ya sanarda karin albashi ga Dagatai dake daukacin masarautu uku dake fadin karamar hukumar Kauru.
Jami’in yada labarai na Karamar Hukumar, Alh Sani Yahaya, ya furta cewa kodayake shugaban bai fadi yawan karin da aka yi ba, sai dai hakan ya zama wajibi domin karfafa musu gwiwar gudanarda ayyukansu a matsayinsu na jagororin wanzar da zaman lafiya da tabbatarda hadin kai.
Bashir Dawaki ya yabawa Dagatai wadanda su ke kusa da al’uma a matakin farko bisa gudunmuwarsu na cigaban yankin, ya bukacesu su kara himma ta hanyar taimakawa jami’an tsaro wajen kawarda miyagun ayyuka a tsakanin al’uma.
Ya kuma gargadi masu hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba a yankin, su nemi iznin gwamnati kafin aikata hakan ko kuma su fuskanci hukunci.
A jawabin Dagacen Garin Kagadama dake gundumar Kauru Alh Umar Kasimu ya nuna jin dadinsa bisa wannan yunkuri ya yi alkawarin cigaba da zage damtse wajen tabbatarda zaman lafiya a yankunansu
Yusuf Zubairu Kauru
-
Labarai4 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi5 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha5 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai5 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai5 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai5 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai3 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai5 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar