Connect with us

Labarai

Saqafatu Movement Foundation Ta Raba Kayan Sallah Ga Marayu.

Published

on

 

Kungiyar Saqafatu Movement Foundation ta raba kayayyakin Sallah ga marayu na dubban naira domin samun falalar wannan wata mai albarka na Ramadan.

Shugabar kungiyar, Malama Asiya Ado Yakasai ta sanarda hakan yayin taron rabon kayayyakin da ya gudana a harabar Masallacin Saqafa dake Barnawa Kaduna.

Ta ce, shekaru 10 kenan da kungiyar ta shafe wajen hidimar baiwa marayu kayan Sallah a irin wannan lokacin na azumin watan Ramadan domin samun falalarsa.

Malama Asiya Ado Yakasai ta nemi gwamnatin da masu ruwa da tsaki su taimaka wa marayu da mabukata musamman a wannan lokaci na matsin tattalin arzikin Kasan nan.

Da take tsokaci, Uwar kungiyar Saqafatu Movement Foundation, Malama Hafsat Yahaya Misau, ta ce, kungiyar tana baiwa marayu 160 kayan Sallah kowace shekara, inda a bana ta baiwa marayu 90 kadai, sakamakon wahalar tsadar rayuwa da ake fama da shi a yanzu.

Ta yi kira ga gwamnati da mawadata su tallafawa kungiyar wajen habaka ayyukanta na alkhairi domin samun tsira a gobe kiyama.

Da yake jawabi a wajen taron, Hakimin Barnawa, Alhaji Kabiru Zubair ya yabawa aikin alkhairin da kungiyar ke gudanarwa duk shekara na taimakawa Marayu.

Ya tunatarda al’uma akan falalar taimakawa Marayu tareda addu’ar Allah Ya sanyawa kungiyar lada a mizani.

Daya daga cikin marayun da suka samu tallafin kayan Sallah Zainab Hussaini ta yi addu’ar Allah Ya cigaba da tallawa kungiyar akan irin hidimar da suke yi ma Marayu.

A wurin taron, an rabawa marayu maza da mata 90 kayan Sallah da suka kunshi atamfofi da shadda da yadi.

Khadija Kubau

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai16 hours ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai17 hours ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai18 hours ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi19 hours ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai2 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai2 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai3 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai3 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai3 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara