Connect with us

Kasuwanci

CBN Ya Karawa Bankuna Jarin Da Za Su Mallaka Zuwa ₦500bn

Published

on

 

Babban Bankin Najeriya (CBN), ya kara adadin kuɗin da bankunan kasuwanci za su mallaka a matsayin jari zuwa Naira biliyan 500.

CBN, ya ce dole ne kowane banki da ke hada-hada har a ƙasashen ƙetare ya kasance yana da jarin da bai gaza Naira biliyan 500 ba.

Wannan na kunshe ne cikin wata takardar da daraktan sashen tsare-tsare da sanya ido kan ka’idojin kudi, Haruna Mustafa, ya sanya wa hannu.

CBN, ya bai wa bankunan kasuwanci da sauran cibiyoyin hada-hadar kudi wa’adin watanni 24 domin cika wannan ka’ida.

Wannan wa’adi zai fara aiki daga ranar 1 ga watan Afrilu, 2024, zuwa watan 31 ga Maris, 2026.

Bankunan da hada-hadarsu iya Najeriya ta tsaya, na buƙatar mafi ƙarancin jari na Naira biliyan 200 domin cikar ka’idar da CBN ya gindaya.

Kazalika, sanarwar ta bayyana cewa ya zama wajibi bankunan da ke aiki a yankunan kasar nan su zama suna da jarin da bai gaza Naira biliyan 50 ba.

 

Ya kuma bayyana cewa bankin da ke son ya rika aiki a fadin Najeriya ba tare da karbar kudin ruwa ba na bukatar jari na Naira biliyan 20.

Bankin da zai rika aiki a wani yanki guda na kasar nan, na bukatar jarin da bai gaza biliyan 10 ba.

Daka karshe, sanarwar ta bai wa bankuna shawarar hadewa domin tabbatar da samun jari mai kauri da kyautata ayyuka ga abokan hulɗarsu.

 

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai2 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai2 hours ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Labarai15 hours ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai3 days ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Fasaha3 days ago

An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar

Kungiyar Malaman Jami’ar Jihar Sakkwato ASUU-SSU ta yi kira ga gwamnatin Jihar ta duba halin da kungiyar ke ciki da...

Kasuwanci3 days ago

Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

  Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin...

Ilimi3 days ago

Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark,...

Labarai6 days ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu. Jakadan...

Labarai1 week ago

Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar...

Mafi Shahara