Labarai
An Karrama Dan Agajin da ya Tsinci Fiye da Naira Miliyan 100 ya Mayar
Ƙungiyar Izala ta ƙasa, JIBWIS ta karrama wani matashin ɗan agaji da ya tsinci kuɗi sama da naira miliyan 100, sannan ya mayar da su.
Cikin wani sako da ƙungiyar reshen jihar Bauchi ta wallafa a shafinta na Facebook, ta ce matashin ɗan agajin mai suna Salihu AbdulHadi Kankia, ya taka rawar gani, wanda ya kai a jinjina masa.
A wurin rufe taron ƙara wa juna sani na malamai masu gabatar da tafsiri, Daraktan Agaji na ƙasa Injiniya Mustapha Imam Sitti ya gabatar da matashin wanda ya tsinci jaka cike da makudan kuɗi da suka kai sama da naira miliyan 100 a Kankia da ke jihar Katsina.
”Salihu ya ɓoye kuɗin a gida, sannan ya garzaya zuwa ofishin ƴansanda ya sanar musu cewa ya tsinci jaka a yi cigiya wa al’umma amma jakar tana wurinsa”, kamar yadda sanarwar ta bayyana.
Kan wannan abin a yaba ne ƙungiyar ta Izala ta karrama matashin da lambar yabo tare da ba shi kyautar kujerar Hajjin bana.
”Sannan kuma Hon. Abdulmalik Zannan Bangudu (Ɗan Agaji kuma Dan Majalisa a Jihar Zamfara) ya bashi kyautar miliyan biyu”, kamar yadda sanarwar ta bayyana.
Sanarwar ta ƙara da cewa gwamnan Jihar Bauchi, Bala Abdulkadir Muhammed ya ba shi kyautar mota kirar bas don ya kama sana’a..
Tsintar makudan kuɗi a kuma mayar da su musamman a wannan yanayi da ake ciki na matsin rayuwa, abin a yaba ne.
Lamarin dai ya sa matashin ya samu kyaututtuka masu ɗimbin yawa a ciki da wajen jihar.
-
Fasaha6 days ago
Shugaba Tinubu Ya Kaddamar Da Kamfanin Sarrafa Sinadarin Batira a Lafiya
-
Ilimi3 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Labarai2 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai6 days ago
Mbappe ya sanar da cewa zai bar PSG a karshen kaka
-
Fasaha3 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai3 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai3 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai3 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana