Labarai
Hukumar Yaki Da Rashawa Ta Kano Ta Sake Gurfanar Da Ganduje Gaban Kuliya
Hukumar yaki da cin hanci da rashawa da sauraron korafe-korafen jama’a ta jihar Kano ta shigar da sabbin tuhume-tuhume kan almundahana a kan tsohon gwamnan jihar Dr. Abdullahi Ganduje.
Shugaban Hukumar, Muhuyi Magaji ne ya bayyana hakan a shirin da yayi a wani gidan talabijin mai zaman kasa a ranar Talata, inda ya zargi gwamnatin Ganduje da karkatar da kudaden al’umma.
Ya bayyana cewa, bincike ya nuna yadda aka karkatar da naira biliyan hamsin da dayada miliyan dari uku na kudaden kananan hukumomi zuwa wasu asusun ajiya da basu da hurumin karbar irin wadannan kudaden.
A cewar Muhuyi, gwamnatin Ganduje na cire naira biliyan 1 a duk wata daga asusun jihar ba bisa ka’ida ba.
Ya kuma yi ikirarin cewa, an zuba Naira biliyan 4 ga asusun wani kamfanin noma daga asusun tattara harajin jihar ba tare da wani dalili ba.
-
Labarai3 days ago
Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa
-
Labarai6 days ago
Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano
-
Fasaha3 days ago
An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar
-
Labarai20 hours ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa
-
Kasuwanci3 days ago
Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno
-
Labarai6 hours ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Ilimi3 days ago
Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert