Labarai
‘Yan Fashin Tekun Somalia Sun Sako Jirgin Bangladesh Bayan Karbar Kudin Fansa
![](https://radionigeriakaduna.gov.ng/hausa/wp-content/uploads/2024/04/AP24030241045609.webp)
‘Yan fashin tekun Somalia sun sako wani jirgin ruwan dakon kaya mai tutar Bangladesh tare da ma’aikatansa 23 a yau lahadi, bayan da masu jirgin suka biya kudin fansa.
Jirgin ruwan MV Abdullah wanda ke jigilar kusan tan dubu hamsin da biyar na kwal daga kasar Mozambique zuwa Hadaddiyar Daular Larabawa, wasu gungun ‘yan fashin teku da dama ne suka shiga da shi a nisan kilomita 1,000 daga gabar tekun Somalia wata guda da ya gabata.
“Mun cimma yarjejeniya da ‘yan fashin,” in ji Mizanul Islam, na kamfanin SR Shipping, mallakin kungiyar KSRM ta Bangladesh.
A cikin watan Maris, dakarun sa kai na India sun kutsa cikin jirgin ruwan Malta MV Ruen, wanda ‘yan fashin tekun Somalia ke rike da shi tun watan Disambar 2023. Wannan dai shi ne nasara na farko da aka samu na fashin teku a gabar tekun Somalia tun shekara ta 2017.
Ma’aikatan jirgin su 17, ‘yan Bama mutum 9, da ‘yan Bulgaria 7 da kuma dan Angola guda, an ceto su ba tare da wani rauni ba, sannan an kai ‘yan fashin 35 zuwa Bombay na kasar India domin gurfanar da su a gaban Kuliya.
-
Labarai7 days ago
Al’ummar Kauru Na Cikin Zullumi Bayan Lalacewar Gadar Da Ta Hadasu Da sauran Al’ummomin Jihar Kaduna
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Harkar Noma A Yobe
-
Labarai2 days ago
Sanatocin Arewa Sun Jinjinawa Tinubu Bisa Amincewa Da Kafa Hukumar Raya Arewa Maso Yamma
-
Kasuwanci4 days ago
An Shawarci Matasan Jihar Niger Su Guji Shiga Zanga-Zangar Babu Gaira Babu Dalili
-
Labarai4 days ago
Zanga Zanga: Gwamnati Ta Baiwa Matasa Tabbacin Daukan Bukatun Su Da Mahimmanci
-
Labarai3 days ago
‘Yan Jaridan Kenya Za Su Yi Zanga-Zangar Adawa Da Cin Zalin ‘Yansanda
-
Labarai5 days ago
Gwamnatin Kano Za Ta Samar Da Kananan Jiragen Ruwa A Kananan Hukumomi 3
-
Labarai4 days ago
Taurarin Finafinan Hausa Na Alhinin Rasuwar Sulaiman Alaka