Labarai
‘Yan Fashin Tekun Somalia Sun Sako Jirgin Bangladesh Bayan Karbar Kudin Fansa
‘Yan fashin tekun Somalia sun sako wani jirgin ruwan dakon kaya mai tutar Bangladesh tare da ma’aikatansa 23 a yau lahadi, bayan da masu jirgin suka biya kudin fansa.
Jirgin ruwan MV Abdullah wanda ke jigilar kusan tan dubu hamsin da biyar na kwal daga kasar Mozambique zuwa Hadaddiyar Daular Larabawa, wasu gungun ‘yan fashin teku da dama ne suka shiga da shi a nisan kilomita 1,000 daga gabar tekun Somalia wata guda da ya gabata.
“Mun cimma yarjejeniya da ‘yan fashin,” in ji Mizanul Islam, na kamfanin SR Shipping, mallakin kungiyar KSRM ta Bangladesh.
A cikin watan Maris, dakarun sa kai na India sun kutsa cikin jirgin ruwan Malta MV Ruen, wanda ‘yan fashin tekun Somalia ke rike da shi tun watan Disambar 2023. Wannan dai shi ne nasara na farko da aka samu na fashin teku a gabar tekun Somalia tun shekara ta 2017.
Ma’aikatan jirgin su 17, ‘yan Bama mutum 9, da ‘yan Bulgaria 7 da kuma dan Angola guda, an ceto su ba tare da wani rauni ba, sannan an kai ‘yan fashin 35 zuwa Bombay na kasar India domin gurfanar da su a gaban Kuliya.
-
Labarai3 days ago
Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa
-
Labarai6 days ago
Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano
-
Fasaha4 days ago
An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar
-
Labarai13 hours ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Labarai1 day ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa
-
Kasuwanci4 days ago
Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno
-
Ilimi4 days ago
Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert