Labarai
Ana Gudanar da Zaɓen Shugaban Kasar Senegal
Yan ƙasar Senegal na kaɗa ƙuri’a ranar Lahadi a zaɓen shugaban ƙasar bayan shekaru uku ana tayar da jijiyoyin siyasa sakamakon tuhumar da aka yi wa jagoran ƴan hamayya Ousmane Sonko da kuma fargabar da aka yi cewa shugaban ƙasar zai tsawaita wa’adin mulkinsa.
Ƴan takara 19 ne za su fafata domin neman wanda zai maye gurbin Shugaba Macky Sall, wanda zai sauka daga mulki bayan ya kammala wa’adi biyu.
Mutum miliyan 7.3 ne suka yi rajista a zaɓen sai dai ana ganin fafatawar za ta fi zafi tsakanin ɗan takarar gamayyar jam’iyyu masu mulki firaiminista Amadou Ba da babban ɗan hamayya Bassirou Diomaye Faye.
Dukansu sun taɓa aiki a hukumar karɓar haraji ta ƙasar, sai dai yanzu kowannensu yana da manufofi da suka sha bamban. Ba, mai shekara 62, ya yi alƙawarin ci gaba da tsarin da shugaba mai ci yake kai, yayin da Faye, mai shekara 43 ya sha alwashin kawo gagarumin sauyi.
Kowannensu ya bugi ƙirji cewa zai lashe zaɓen a zagayen farko — sai dai akwai yiwuwar ta tafi zagaye na biyu, domin kuwa akwai ƴan takara 15 a zaɓen, ciki har da mace guda ɗaya.
Za a rufe rumfunan zaɓe ne da misalin ƙarfe shida na yamma a agogon Dakar kuma ana sa ran soma sanar da sakamakon zaɓen da tsakar dare.
Ɗaruruwan masu jami’ai daga Tarayyar Afirka da ECOWAS da kuma Tarayyar Turai ne za su sanya ido kan zaɓen.
-
Labarai7 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Labarai19 hours ago
NAHCON Ta Jinjinawa Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Bisa Shirye-shiryen Hajjin Bana
-
Ilimi5 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura
-
Labarai19 hours ago
Amurka Ta Dakatar Da Kudurin Kai Jirgin Bama-Bamai Zuwa Isra’ila
-
Labarai5 days ago
An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya
-
Fasaha2 days ago
Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno
-
Fasaha2 days ago
Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet
-
Kasuwanci2 days ago
CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati