Connect with us

Labarai

Shugabannin ECOWAS na Gudanar da Taro Kan Matsalar Yankin

Published

on

Shugabannin ƙasashen ƙungiyar ECOWAS ko CEDEO  a yau Asabar za su gudanar da taro a Abuja babban birnin Najeriya.

Yankin na yammacin Afrika na fuskantar barazanar rashin haɗin kai tun bayan da ƙasashen Burkina Faso da Mali da Nijar suka bayyana aniyarsu ta ficewa daga ƙungiyar.

Yayin da a ɗayan ɓangaren ƙasar Senegal ke fama da dambarwar siyasa sakamakon matakin shugaba Macky Sall na ɗage babban zaɓen ƙasar.

Ana saran dai a wanann taro ƙungiyar za ta lalubo mafita kan wadanan matsaloli da suka mamaye yankin.

Wannan zai iya zama gagarumin ƙalubale da kungiyar ke fuskanta tun bayan kafata shekaru 50 da suka gabata.

Hudu cikin mambobin ƙungiyar 15 yanzu haka na ƙarƙashin shugabancin soji.

Taron kuma na zuwa ne bayan da tsohon shugaban Najeriya na mulkin soja, kuma shugaba ɗaya tilo da ya rage cikin waɗanda suka kafa ƙungiyar ta ECOWAS ko CEDEO, Janar Yakubu Gowon mai ritaya, ya yi kira da a gaggauta ɗage duk wani takunkumin da aka ƙaƙaba wa ƙasashen Gini da Burkina Faso da Mali da kuma Nijar.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai3 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai3 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai3 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi3 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai4 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai4 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai5 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai5 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai5 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara