Connect with us

Labarai

NAFDAC Ta Rufe Shagunan Magani 1321 A Kano

Published

on

Hukumar da ke Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Kasa NAFDAC reshen Jihar Kano tare da hadin gwiwar Hukumar da ke Kula da Magunguna ta Kasa sun rufe shagunan magani 1321 da ke Malam Kato da Mai Kari Plaza da kuma cikin Kasuwar Sabon Gari a jihar.

Shugaban Hukumar a Jihar Kano, Kashm Ibrahim ya ce, sun rufe shagunan ne don ganin masu maganin sun bi doka ta hanyar komawa Kasuwar Dangwauro wacce Gwamnatin Jihar ta tanadar musu.

 

Haka kuma, Kashin Ibrahim ya ce za a ci gaba da samar da wasu shagunan a cikin kasuwar don magance matsalar da ‘yan maganin ke dogaro da ita cewa rashin isassun shagunan ne ya hana su komawa kasuwar.

A cewarsa, magani abu ne da ya shafi rayuwar mutane don haka ba za a dauke shi da wasa ba.

Sai dai masu maganin ta hanyar kungiyarsu ta NAPPMED sun bayyana cewa suma sun rufe shagunansu tare da shiga yajin aikin sayar da magani har sai baba ta gani.

Shugaban Kungiyar Alhaji Muhammad Musbahu Khalid ya bayyana cewa, sun rufe shagunansu ne don gwamnati ta san amfaninsu a Jihar Kano.

Ya kuma musanta batun da ake yi cewa ‘yan kabilar Ibo ne masu sana’ar magani a Kano, “wannan zance ne mara tushe kuma zalinci ne. Muna so al’ummar jihar manya da kanana su sani an yi haka ne saboda zalunci.”

A cewarsa, sabon wurin da ake so a koma na Dangwauro ba na gwamnati ba ne, kawai na wasu ne domin tsawwala wa ’yan kasuwar magani.

Idan za a iya tunawa a ranar Juma’ar da ta gabata ce Babbar Kotun Tarayya da ke zamanta a Jihar Kano karkashin jagorancin Mai sharia Simon Amobeda ta umarci manyan dilolin masu maganin da su koma Kasuwar Dangwauro don ci gaba da kasuwancinsu.

Hukuncin kotun shi ya kawo karshen takaddamar da aka dauki tsawon shekara biyar ana yi tsakanin bangarorin biyu na hukumar da ke kula da magunguna ta kasa da kuma kungiyar ’yan maganin.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai17 hours ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai18 hours ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai19 hours ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi20 hours ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai2 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai2 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai3 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai3 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai3 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara