Labarai
Matasa sun fara hakura da shan miyagun kwayoyi: – NDLEA
Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA reshen jihar Kwara, ta ce za ta kara karfafa matasa su shiga wasannin motsa jiki domin rage sha da safarar miyagun kwayoyi a tsakanin su.
Kwamandan NDLEA na jihar, Mohammed Ibrahim ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da mambobin kungiyar marubuta wasanni (SWAN) a Ilorin babban birnin jihar Kwara.
A cewarsa, sun dauki matakin bayan kalubalen da ake fuskanta a baya-bayan nan na aikin ‘yan masu safarar miyagun kwayoyi a jihar.
Ya ce kamar yadda matasa ke amfani da muggan kwayoyi yana sa su kara kaimi wajen yaki da wannan mummunan dabi’a.
Kwamanda Ibrahim ya nuna damuwarsa kan zargin da ake yi na sayar da miyagun kwayoyi da da masu kula da ‘yan wasa ke yi.
Ya kuma ce hukumarsa ta samu a nasara a baya-bayan nan ne na samun hukuncin daurin rai da rai kan wani koci da aka kama yana sayar da kwayoyi ga matasa ‘yan wasa da yake kula da su.
A nasa jawabin shugaban kungiyar marubuta wasanni ta Najeriya SWAN reshen jihar Kwara, Ayodeji Ismail ya bayyana cewa marubutan wasanni suna da masaniya kan illolin da shan miyagun kwayoyi ke haifarwa.
Ya kuma bada tabbacin cewa kungiyar zata sake horas da ‘ya’yan kungiyar domin bayar da rahoton illolin shaye-shayen miyagun kwayoyi a tsakanin matasa.
COVALI MUHAMMAD RABIU/Wababe
-
Labarai6 days ago
Wajibi Ne a kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Kano Nan da Watanni 14 – FG
-
Labarai5 days ago
Hukumar Shige da Fice Ta Gargadi Jama’a Kan Sabuwar Kungiya Achad Life Mission
-
Labarai2 days ago
Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Ta Samar Da Masauki Na Alfarma Ga Alhazan Jihar
-
Kasuwanci6 days ago
Na Biya Dala Dubu 3 Don a Asirce Mijina Ya Mayar da Auren Mu – Bose
-
Labarai4 days ago
Gwamnatin Neja Ta Haramtawa Motocin Da Suka Fito Daga Hanyar Maje Bin Gadar Dikko
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Jihar Kano Ta Dawo Da Ayyukan Ma’aikatar Yada Labarai
-
Labarai5 days ago
Majalisar Dattijai Ta Bukaci Karfafa Jarin Bankin Lamunin Gidaje Na Tarayya
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Nijar ta soke biyan kudaden PTA a Makarantun Gwamnati