Connect with us

Labarai

Matasa sun fara hakura da shan miyagun kwayoyi: – NDLEA

Published

on

Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA reshen jihar Kwara, ta ce za ta kara karfafa matasa su shiga wasannin motsa jiki domin rage sha da safarar miyagun kwayoyi a tsakanin su.

 

Kwamandan NDLEA na jihar, Mohammed Ibrahim ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da mambobin kungiyar marubuta wasanni (SWAN) a Ilorin babban birnin jihar Kwara.

 

A cewarsa, sun dauki matakin bayan kalubalen da ake fuskanta a baya-bayan nan na aikin ‘yan  masu safarar miyagun kwayoyi a jihar.

 

Ya ce kamar yadda matasa ke amfani da muggan kwayoyi yana sa su kara kaimi wajen yaki da wannan mummunan dabi’a.

 

Kwamanda Ibrahim ya nuna damuwarsa kan zargin da ake yi na sayar da miyagun kwayoyi da da masu kula da ‘yan wasa ke yi.

 

Ya kuma ce hukumarsa ta samu a nasara a baya-bayan nan ne na samun hukuncin daurin rai da rai kan wani koci da aka kama yana sayar da kwayoyi ga matasa ‘yan wasa da yake kula da su.

 

A nasa jawabin shugaban kungiyar marubuta wasanni ta Najeriya SWAN reshen jihar Kwara, Ayodeji Ismail ya bayyana cewa marubutan wasanni suna da masaniya kan illolin da shan miyagun kwayoyi ke haifarwa.

 

Ya kuma bada tabbacin cewa kungiyar zata sake horas da ‘ya’yan kungiyar domin bayar da rahoton illolin shaye-shayen miyagun kwayoyi a tsakanin matasa.

COVALI MUHAMMAD RABIU/Wababe

 

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai7 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai7 hours ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Labarai20 hours ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai3 days ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Fasaha3 days ago

An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar

Kungiyar Malaman Jami’ar Jihar Sakkwato ASUU-SSU ta yi kira ga gwamnatin Jihar ta duba halin da kungiyar ke ciki da...

Kasuwanci3 days ago

Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

  Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin...

Ilimi3 days ago

Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark,...

Labarai6 days ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu. Jakadan...

Labarai1 week ago

Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar...

Mafi Shahara