Labarai
Matasa sun fara hakura da shan miyagun kwayoyi: – NDLEA
![](https://radionigeriakaduna.gov.ng/hausa/wp-content/uploads/2024/04/d58d5a32-183f-42f5-a4f2-456ab9ac62d5.jpeg)
Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA reshen jihar Kwara, ta ce za ta kara karfafa matasa su shiga wasannin motsa jiki domin rage sha da safarar miyagun kwayoyi a tsakanin su.
Kwamandan NDLEA na jihar, Mohammed Ibrahim ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da mambobin kungiyar marubuta wasanni (SWAN) a Ilorin babban birnin jihar Kwara.
A cewarsa, sun dauki matakin bayan kalubalen da ake fuskanta a baya-bayan nan na aikin ‘yan masu safarar miyagun kwayoyi a jihar.
Ya ce kamar yadda matasa ke amfani da muggan kwayoyi yana sa su kara kaimi wajen yaki da wannan mummunan dabi’a.
Kwamanda Ibrahim ya nuna damuwarsa kan zargin da ake yi na sayar da miyagun kwayoyi da da masu kula da ‘yan wasa ke yi.
Ya kuma ce hukumarsa ta samu a nasara a baya-bayan nan ne na samun hukuncin daurin rai da rai kan wani koci da aka kama yana sayar da kwayoyi ga matasa ‘yan wasa da yake kula da su.
A nasa jawabin shugaban kungiyar marubuta wasanni ta Najeriya SWAN reshen jihar Kwara, Ayodeji Ismail ya bayyana cewa marubutan wasanni suna da masaniya kan illolin da shan miyagun kwayoyi ke haifarwa.
Ya kuma bada tabbacin cewa kungiyar zata sake horas da ‘ya’yan kungiyar domin bayar da rahoton illolin shaye-shayen miyagun kwayoyi a tsakanin matasa.
COVALI MUHAMMAD RABIU/Wababe
-
Labarai7 days ago
Al’ummar Kauru Na Cikin Zullumi Bayan Lalacewar Gadar Da Ta Hadasu Da sauran Al’ummomin Jihar Kaduna
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Harkar Noma A Yobe
-
Labarai2 days ago
Sanatocin Arewa Sun Jinjinawa Tinubu Bisa Amincewa Da Kafa Hukumar Raya Arewa Maso Yamma
-
Kasuwanci4 days ago
An Shawarci Matasan Jihar Niger Su Guji Shiga Zanga-Zangar Babu Gaira Babu Dalili
-
Labarai4 days ago
Zanga Zanga: Gwamnati Ta Baiwa Matasa Tabbacin Daukan Bukatun Su Da Mahimmanci
-
Labarai3 days ago
‘Yan Jaridan Kenya Za Su Yi Zanga-Zangar Adawa Da Cin Zalin ‘Yansanda
-
Labarai5 days ago
Gwamnatin Kano Za Ta Samar Da Kananan Jiragen Ruwa A Kananan Hukumomi 3
-
Labarai4 days ago
Taurarin Finafinan Hausa Na Alhinin Rasuwar Sulaiman Alaka