Connect with us

Labarai

Matasa sun fara hakura da shan miyagun kwayoyi: – NDLEA

Published

on

Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA reshen jihar Kwara, ta ce za ta kara karfafa matasa su shiga wasannin motsa jiki domin rage sha da safarar miyagun kwayoyi a tsakanin su.

 

Kwamandan NDLEA na jihar, Mohammed Ibrahim ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da mambobin kungiyar marubuta wasanni (SWAN) a Ilorin babban birnin jihar Kwara.

 

A cewarsa, sun dauki matakin bayan kalubalen da ake fuskanta a baya-bayan nan na aikin ‘yan  masu safarar miyagun kwayoyi a jihar.

 

Ya ce kamar yadda matasa ke amfani da muggan kwayoyi yana sa su kara kaimi wajen yaki da wannan mummunan dabi’a.

 

Kwamanda Ibrahim ya nuna damuwarsa kan zargin da ake yi na sayar da miyagun kwayoyi da da masu kula da ‘yan wasa ke yi.

 

Ya kuma ce hukumarsa ta samu a nasara a baya-bayan nan ne na samun hukuncin daurin rai da rai kan wani koci da aka kama yana sayar da kwayoyi ga matasa ‘yan wasa da yake kula da su.

 

A nasa jawabin shugaban kungiyar marubuta wasanni ta Najeriya SWAN reshen jihar Kwara, Ayodeji Ismail ya bayyana cewa marubutan wasanni suna da masaniya kan illolin da shan miyagun kwayoyi ke haifarwa.

 

Ya kuma bada tabbacin cewa kungiyar zata sake horas da ‘ya’yan kungiyar domin bayar da rahoton illolin shaye-shayen miyagun kwayoyi a tsakanin matasa.

COVALI MUHAMMAD RABIU/Wababe

 

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai14 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Bada Lamunin Sama Da Naira Biliyan 3 Ga Hukumar Alhazan Jihar

Majalisar zartaswa ta jihar Jigawa ta amince da bukatar hukumar Alhazai ta jihar na naira biliyan uku da miliyan dari...

Labarai16 hours ago

An Tsinci Gawar Wani Mutum A Cikin Rijiya A Karamar Hukumar Gezawa

Al’ummar kauyen Babawa da ke karamar hukumar Gezawa a Kano sun shiga cikin firgici bayan da aka tsinci wani mutum...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Ta Samar Da Masauki Na Alfarma Ga Alhazan Jihar

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce ta samar wa Alhazan Jiha katafaren masauki na alfarma  a kusa...

Labarai3 days ago

Hukumar Alhazai Ta Kasa Ta Sanar Da Kudin Aikin Hajjin Bana

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da kudin aikin Hajjin shekarar 2025. Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa...

Labarai3 days ago

Sanata Yari Ya Bada Gudummawar Kudi Ga Wadanda Harin Sama Ya Shafa A Maradun

Tsohon Gwamnan Jihar Zamfara, Abdul’azeez Yari Abubakar, ya bayar da naira miliyan 23 da kuma buhuna 105 na kayan abinci...

Ilimi3 days ago

Gwamna Namadi Tare Da Hadin Gwiwar Kasar Qatar Sun Samar Da Cibiyar Bunkasa Ilimi A Jigawa

Gwamna Mallam Umar Namadi ya kaddamar da Cibiyar Al’amuran  Addinin Musulunci a kauyen Babbar Riga dake karamar hukumar Malam-Madori a...

Labarai3 days ago

Shugaba Tinubu Ya Jajantawa Al’ummar Jihar Neja Bisa Iftila’in Fashewar Tankar Mai

Shugaba Bola Tinubu ya bayyana alhininsa kan fashewar tankar mai da ta yi sanadin mutuwar mutane sama da 80 tare...

Labarai4 days ago

Gwamnatin Neja Ta Haramtawa Motocin Da Suka Fito Daga Hanyar Maje Bin Gadar Dikko

Gwamnatin Jihar Neja ta ba da umarnin hana motocin da suka  fito daga Maje hawa gadar Dikko. Gwamnan jihar Mohammed...

Labarai5 days ago

Hukumar Shige da Fice Ta Gargadi Jama’a Kan Sabuwar Kungiya Achad Life Mission

Hukumar Shige da Fice ta Kasa (NIS) ta bayyana damuwa kan bullar wata sabuwar kungiya mai suna Achad Life Mission...

Labarai5 days ago

Majalisar Dattijai Ta Bukaci Karfafa Jarin Bankin Lamunin Gidaje Na Tarayya

Majalisar dattawan na shirin yin amfani da bangaren zartaswa na gwamnati kan gaggauta samarda kwakkwaran jari ga babban bankin bayar...

Mafi Shahara