Kasuwanci
Gwamnan Kano Ya Kaddamar Da Rarraba Kayan Agaji Na Ramadan
![](https://radionigeriakaduna.gov.ng/hausa/wp-content/uploads/2024/04/050b8555-be52-4f0c-92bd-1da6dc4bbccb.jpeg)
Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano ya kaddamar da rabon kayan abinci na Ramadan karo na hudu ga mabukata da marasa galihu a kananan hukumomin jihar 44, tare da gargadi kan karkatar da kayan abinci.
Yusuf ya kaddamar da rabon ne a masana’antar shinkafa ta Tiamin da ke karamar hukumar Dawakin Kudu.
Da yake jawabi a lokacin bikin, gwamnan ya gargadi masu kula da rabon kayan agajin da su guji karkatar da su, yana mai jaddada cewa duk wanda aka samu yana karkatar da su za a hukunta shi kamar yadda doka ta tanada.
“Na rantse da Allah duk wanda aka samu yana karkatar da kayan agajin za a yi hukunci mai tsauri kuma bisa doka, wannan gwamnati ba za ta bari masu zagon kasa su sha ba,” inji shi.
Gwamnan ya ce dalilin wannan tallafin shi don saukaka wahalhalun da ake fuskanta, a lokacin azumin watan Ramadan.
Ya ce za a raba buhunan kayan masarufi 224,440 ga gundumomin Sanatoci uku da ke jihar domin ci gaba da rabawa wadanda za su ci gajiyar shirin.
Ya kuma nemi afuwar al’ummar jihar kan hakurin da suka nuna a lokacin da ake sarrafa shinkafar da buhu domin rabawa.
Gwamna Yusuf ya ce gwamnatinsa za ta ci gaba da shiga tsakani “har sai an kawar da yunwa a tsakanin mutanenmu.”
Ya godewa gidauniyar Aliko Dangote da sauran kungiyoyi da daidaikun jama’a da suka raba nasu kayan agajin ga mabukata a cikin wannan wata mai alfarma, ya kuma yi addu’ar Allah ya saka musu da alheri.
Tun da farko, Shugaban Kwamitin Rarraba tallafin, Dakta Abdullahi Baffa Bichi, ya ce wannan rabon shi ne na hudu a cikin shirin rabon kayan abinci ga jama’a.
Bichi, wanda kuma shi ne sakataren gwamnatin jihar, ya yabawa gwamna Yusuf bisa wannan karimcin, wanda yace zai rage musu wahalhalu.
ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO/Wababe
-
Labarai7 days ago
Al’ummar Kauru Na Cikin Zullumi Bayan Lalacewar Gadar Da Ta Hadasu Da sauran Al’ummomin Jihar Kaduna
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Harkar Noma A Yobe
-
Labarai2 days ago
Sanatocin Arewa Sun Jinjinawa Tinubu Bisa Amincewa Da Kafa Hukumar Raya Arewa Maso Yamma
-
Kasuwanci4 days ago
An Shawarci Matasan Jihar Niger Su Guji Shiga Zanga-Zangar Babu Gaira Babu Dalili
-
Labarai4 days ago
Zanga Zanga: Gwamnati Ta Baiwa Matasa Tabbacin Daukan Bukatun Su Da Mahimmanci
-
Labarai5 days ago
Gwamnatin Kano Za Ta Samar Da Kananan Jiragen Ruwa A Kananan Hukumomi 3
-
Labarai3 days ago
‘Yan Jaridan Kenya Za Su Yi Zanga-Zangar Adawa Da Cin Zalin ‘Yansanda
-
Labarai4 days ago
Taurarin Finafinan Hausa Na Alhinin Rasuwar Sulaiman Alaka