Connect with us

Kasuwanci

Gwamnan Kano Ya Kaddamar Da Rarraba Kayan Agaji Na Ramadan

Published

on

 

Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano ya kaddamar da rabon kayan abinci na Ramadan karo na hudu ga mabukata da marasa galihu a kananan hukumomin jihar 44, tare da gargadi kan karkatar da kayan abinci.

 

Yusuf ya kaddamar da rabon ne a masana’antar shinkafa ta Tiamin da ke karamar hukumar Dawakin Kudu.

 

Da yake jawabi a lokacin bikin, gwamnan ya gargadi masu kula da rabon kayan agajin da su guji karkatar da su, yana mai jaddada cewa duk wanda aka samu yana karkatar da su za a hukunta shi kamar yadda doka ta tanada.

 

“Na rantse da Allah duk wanda aka samu yana karkatar da kayan agajin za a yi hukunci mai tsauri kuma bisa doka, wannan gwamnati ba za ta bari masu zagon kasa su sha ba,” inji shi.

 

Gwamnan ya ce dalilin wannan tallafin shi don saukaka wahalhalun da ake fuskanta, a lokacin azumin watan Ramadan.

 

Ya ce za a raba buhunan kayan masarufi 224,440 ga gundumomin Sanatoci uku da ke jihar domin ci gaba da rabawa wadanda za su ci gajiyar shirin.

 

Ya kuma nemi afuwar al’ummar jihar kan hakurin da suka nuna a lokacin da ake sarrafa shinkafar da buhu domin rabawa.

 

Gwamna Yusuf ya ce gwamnatinsa za ta ci gaba da shiga tsakani “har sai an kawar da yunwa a tsakanin mutanenmu.”

 

Ya godewa gidauniyar Aliko Dangote da sauran kungiyoyi da daidaikun jama’a da suka raba nasu kayan agajin ga mabukata a cikin wannan wata mai alfarma, ya kuma yi addu’ar Allah ya saka musu da alheri.

 

Tun da farko, Shugaban Kwamitin Rarraba tallafin, Dakta Abdullahi Baffa Bichi, ya ce wannan rabon shi ne na hudu a cikin shirin rabon kayan abinci ga jama’a.

 

Bichi, wanda kuma shi ne sakataren gwamnatin jihar, ya yabawa gwamna Yusuf bisa wannan karimcin, wanda yace zai rage musu wahalhalu.

 

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO/Wababe

 

 

Labarai

Labarai2 hours ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai2 days ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Fasaha3 days ago

An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar

Kungiyar Malaman Jami’ar Jihar Sakkwato ASUU-SSU ta yi kira ga gwamnatin Jihar ta duba halin da kungiyar ke ciki da...

Kasuwanci3 days ago

Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

  Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin...

Ilimi3 days ago

Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark,...

Labarai5 days ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Ilimi5 days ago

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu. Jakadan...

Labarai1 week ago

Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar...

Ilimi1 week ago

Daliban Jihar Kebbi Da Ke Kasashen Waje Za Su Sami Tallafin Naira Miliyan 309

Gwamnatin jihar Kebbi, ta amince da kashe sama da Naira miliyan Dari Uku da Tara, domin biyan tallafin karatu na...

Kasuwanci1 week ago

Kwari Masu Lalata Amfanin Gona Sun Mamaye Gonakin Tumatur A Kano

Shugaban kungiyar manoma ta jihar Kano, AFAN, Abdullahi Maibreadi, ya bukaci gwamnati a dukkan matakai da su taimaka wa manoma...

Mafi Shahara