Connect with us

Kasuwanci

Gwamnan Kano Ya Kaddamar Da Rarraba Kayan Agaji Na Ramadan

Published

on

 

Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano ya kaddamar da rabon kayan abinci na Ramadan karo na hudu ga mabukata da marasa galihu a kananan hukumomin jihar 44, tare da gargadi kan karkatar da kayan abinci.

 

Yusuf ya kaddamar da rabon ne a masana’antar shinkafa ta Tiamin da ke karamar hukumar Dawakin Kudu.

 

Da yake jawabi a lokacin bikin, gwamnan ya gargadi masu kula da rabon kayan agajin da su guji karkatar da su, yana mai jaddada cewa duk wanda aka samu yana karkatar da su za a hukunta shi kamar yadda doka ta tanada.

 

“Na rantse da Allah duk wanda aka samu yana karkatar da kayan agajin za a yi hukunci mai tsauri kuma bisa doka, wannan gwamnati ba za ta bari masu zagon kasa su sha ba,” inji shi.

 

Gwamnan ya ce dalilin wannan tallafin shi don saukaka wahalhalun da ake fuskanta, a lokacin azumin watan Ramadan.

 

Ya ce za a raba buhunan kayan masarufi 224,440 ga gundumomin Sanatoci uku da ke jihar domin ci gaba da rabawa wadanda za su ci gajiyar shirin.

 

Ya kuma nemi afuwar al’ummar jihar kan hakurin da suka nuna a lokacin da ake sarrafa shinkafar da buhu domin rabawa.

 

Gwamna Yusuf ya ce gwamnatinsa za ta ci gaba da shiga tsakani “har sai an kawar da yunwa a tsakanin mutanenmu.”

 

Ya godewa gidauniyar Aliko Dangote da sauran kungiyoyi da daidaikun jama’a da suka raba nasu kayan agajin ga mabukata a cikin wannan wata mai alfarma, ya kuma yi addu’ar Allah ya saka musu da alheri.

 

Tun da farko, Shugaban Kwamitin Rarraba tallafin, Dakta Abdullahi Baffa Bichi, ya ce wannan rabon shi ne na hudu a cikin shirin rabon kayan abinci ga jama’a.

 

Bichi, wanda kuma shi ne sakataren gwamnatin jihar, ya yabawa gwamna Yusuf bisa wannan karimcin, wanda yace zai rage musu wahalhalu.

 

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO/Wababe

 

 

Labarai

Labarai1 day ago

Muna Tare Da Gwamnatin Bola Tinubu – Gamayyar Kungiyoyin Matasan Arewa

Gamayyar Kungiyoyin MatasanJihohin Arewa Na 19 Sun Ce ko kadan ba sa goyon bayan Zanga-zangar, domin Barazana ce Ga Tsaron...

Labarai2 days ago

‘Yansanda Sun Sake Kama Masu Zanga-Zanga 70 A Uganda

An kama masu zanga-zanga da dama wadanda suka halarci wani haramtaccen gangami da aka gudanar a Kampala babban birnin Uganda,...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Wa Masu Shirin Zanga-Zanga Gargadi

Rundunar Tsaron Najeriya ta gargadi masu shirin zanga-zangar yaki da tsadar rayuwa a Najeriya ta ce sojoji ba za su...

Labarai2 days ago

Olympics: ‘Yan Matan Najeriya Za Su Kara Da Na Brazil

A yau Alhamis ne ƙungiyar Super Falcons ta ‘yan ƙwallon matan Najeriya za su kara da takwarorinsu na Brazil a...

Labarai2 days ago

Sanatocin Arewa Sun Jinjinawa Tinubu Bisa Amincewa Da Kafa Hukumar Raya Arewa Maso Yamma

Kungiyar Sanatocin Arewa ta yabawa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu bisa rattaba hannu kan kudirin hukumar raya yankin Arewa maso...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Bukatar Gudanar Da Zaben Kananan Hukumomi

Majalisar zartaswar jihar Jigawa ta amince da bukatar hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar, na gudanar da zaben kananan...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Hukumar Raya Arewa Maso Yamma

Shugaban kasa Bola Tinubu ya rattaba hannu  kan kudirin doka don hanzarta samar da ci gaba a shiyyoyin kasar nan....

Labarai3 days ago

Za’a Fara Wasannin Olympics A Faransa

Yayin da ake dab da fara gasar wasannin motsa jiki ta bazara wato Olympic, ta shekarar 2024 a birnin Paris...

Labarai3 days ago

‘Yan Jaridan Kenya Za Su Yi Zanga-Zangar Adawa Da Cin Zalin ‘Yansanda

Ƴanjarida a ƙasar Kenya za su gudanar da zanga-zanga a faɗin ƙasar domin nuna adawa da zargin cin zalin da...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Rabon Tallafi Ga Kananan ‘Yan Kasuwa A Jigawa

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta bukaci matasa da su guji yin zanga-zanga a kasa. Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ne ya...

Mafi Shahara