Connect with us

Labarai

Tabbatar kana ganin likita akai-akai Don Hana Makanta – Dr. Avar

Published

on

Dokta Gideon Avar, likitan ido, ya jaddada mahimmancin duba lafiyar mutanen da suka kai shekaru arba’in zuwa sama don hana makanta.

 

Kamar yadda Daraktan Likitoci na Cibiyar Ido ta Nobis da ke Jalingo, Jihar Taraba, Dokta Avar ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a asibitin ido na Nobis VIP da ke mil 6.

 

Duk da kalubalen da asibitinsa ke fuskanta, Dokta Avar ya ambata cewa suna sadaukarwa don taimaka wa majiyyata ta hanyar rage farashin kuɗin magani.

 

Ya bayyana cewa galibin ayyukan da suke yi na aikin agaji ne, kuma a wani bangare na ayyukansu na zamantakewar al’umma, sun samar da rijiyoyin burtsatse guda hudu a cikin al’ummar da suke zaune domin samar da ruwan sha kyauta ga mutane.

 

Dokta Avar ya bukaci daidaikun mutane, musamman wadanda suka haura shekaru arba’in da su ba da fifiko wajen duba lafiyar jama’a, domin rigakafin ya fi magani.

 

Ya kuma bayyana cewa ciwon ido da yana ne kan gaba wajen kawo makanta a Najeriya, inda ya ce asibitin na gudanar da aikin tiyatar ido ga mutane kusan dubu 3 a duk shekara.

 

 

Sani Sulaiman/Wababe

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai7 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai8 hours ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Labarai21 hours ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai3 days ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Fasaha3 days ago

An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar

Kungiyar Malaman Jami’ar Jihar Sakkwato ASUU-SSU ta yi kira ga gwamnatin Jihar ta duba halin da kungiyar ke ciki da...

Kasuwanci3 days ago

Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

  Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin...

Ilimi3 days ago

Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark,...

Labarai6 days ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu. Jakadan...

Labarai1 week ago

Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar...

Mafi Shahara