Labarai
Tabbatar kana ganin likita akai-akai Don Hana Makanta – Dr. Avar
Dokta Gideon Avar, likitan ido, ya jaddada mahimmancin duba lafiyar mutanen da suka kai shekaru arba’in zuwa sama don hana makanta.
Kamar yadda Daraktan Likitoci na Cibiyar Ido ta Nobis da ke Jalingo, Jihar Taraba, Dokta Avar ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a asibitin ido na Nobis VIP da ke mil 6.
Duk da kalubalen da asibitinsa ke fuskanta, Dokta Avar ya ambata cewa suna sadaukarwa don taimaka wa majiyyata ta hanyar rage farashin kuɗin magani.
Ya bayyana cewa galibin ayyukan da suke yi na aikin agaji ne, kuma a wani bangare na ayyukansu na zamantakewar al’umma, sun samar da rijiyoyin burtsatse guda hudu a cikin al’ummar da suke zaune domin samar da ruwan sha kyauta ga mutane.
Dokta Avar ya bukaci daidaikun mutane, musamman wadanda suka haura shekaru arba’in da su ba da fifiko wajen duba lafiyar jama’a, domin rigakafin ya fi magani.
Ya kuma bayyana cewa ciwon ido da yana ne kan gaba wajen kawo makanta a Najeriya, inda ya ce asibitin na gudanar da aikin tiyatar ido ga mutane kusan dubu 3 a duk shekara.
Sani Sulaiman/Wababe
-
Labarai3 days ago
Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa
-
Labarai6 days ago
Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano
-
Fasaha3 days ago
An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar
-
Labarai21 hours ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa
-
Kasuwanci3 days ago
Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno
-
Labarai7 hours ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Ilimi3 days ago
Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert