Fasaha
Tinubu Ya Rattaba Hannu Kan Dokar Bai Wa Ɗalibai Rancen Kuɗin Karatu
Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya rattaba hannu a kan dokar bai wa ɗalibai bashin karatu.
Ya sa hannu kan dokar ce a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja a wannan Larabar.
Hakan na ƙunshe cikin wani saƙo da hadiminsa kan zaurukan sada zumunta, Dada Olusegun ya wallafa.
Dokar mai taken kudurin sauya wa dokar bai wa dalibai rancen karatu fasali ta 2024, an samar da ita ne domin kafa asusun tallafa wa ɗaliban makarantun gaba da sakandire.
A watan Nuwambar shekarar da ta wuce ne majalisar dokokin kasar ta amince da kudurin dokar, da ke neman kafa wata gidanauniyar da za ta riƙa ba daliban manyan makarantun kasar bashin kudin makaranta.
Sai dai ƙudirin ya fuskanci tasgaro dangane da wasu mas’aloli da suka shafi tsare-tsaren karɓa da biyan bashin kuɗin, lamarin da ya sanya Tinubu ya sake bitar ƙudirin tare da aike wa majalisa sabuwar buƙatar neman amincewarta.
A ranar 20 ga Maris, Majalisar Dattawa ta zartar da ƙudirin bayan nazarin rahoton kwamitinta da ke da alhakin kula da manyan makarantun da Asusun TETFUND da suka yi la’akari da kudirin.
Karkashin dokar bai wa ɗalibai rancen kuɗin karatu, za a ba da lamuni marar ruwa ga ’yan Najeriya da suka cancanci samun ilimi mai zurfi.
Masu ruwa da tsaki dai sun tabo batutuwan da suka shafi tsarin bayar da rancen kuɗin ga ɗalibai, musamman ma kan abin da ya shafi buƙatun cancanta, hanyoyin samar da kuɗaɗen, hanyoyin miƙa ɗalibai rancen da suka nema da kuma biyan bashin kuɗaɗen da sauran su.
Sabuwar dokar dai ita ce irinta ta farko a Najeriya a cewar Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Kasa, Femi Gbajabiamila.
Gbajabiamila wanda shi ne ya kawo kudurin dokar lokacin yana kakakin majalisa, ya ce dokar za ta inganta kasar domin babu wani yaron Najeriya da za a hana wa damar samun ilmi mai zurfi saboda rashin kuɗi.
Bello Wakili/Wababe
-
Labarai3 days ago
Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa
-
Labarai6 days ago
Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano
-
Fasaha3 days ago
An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar
-
Kasuwanci3 days ago
Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA
-
Labarai15 hours ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno
-
Ilimi3 days ago
Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert
-
Labarai1 hour ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka