Connect with us

Fasaha

Tinubu Ya Rattaba Hannu Kan Dokar Bai Wa Ɗalibai Rancen Kuɗin Karatu

Published

on

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya rattaba hannu a kan dokar bai wa ɗalibai bashin karatu.

Ya sa hannu kan dokar ce a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja a wannan Larabar.

Hakan na ƙunshe cikin wani saƙo da hadiminsa kan zaurukan sada zumunta, Dada Olusegun ya wallafa.

Dokar mai taken kudurin sauya wa dokar bai wa dalibai rancen karatu fasali ta 2024, an samar da ita ne domin kafa asusun tallafa wa ɗaliban makarantun gaba da sakandire.

A watan Nuwambar shekarar da ta wuce ne majalisar dokokin kasar ta amince da kudurin dokar, da ke neman kafa wata gidanauniyar da za ta riƙa ba daliban manyan makarantun kasar bashin kudin makaranta.

Sai dai ƙudirin ya fuskanci tasgaro dangane da wasu mas’aloli da suka shafi tsare-tsaren karɓa da biyan bashin kuɗin, lamarin da ya sanya Tinubu ya sake bitar ƙudirin tare da aike wa majalisa sabuwar buƙatar neman amincewarta.

A ranar 20 ga Maris, Majalisar Dattawa ta zartar da ƙudirin bayan nazarin rahoton kwamitinta da ke da alhakin kula da manyan makarantun da Asusun TETFUND da suka yi la’akari da kudirin.

Karkashin dokar bai wa ɗalibai rancen kuɗin karatu, za a ba da lamuni marar ruwa ga ’yan Najeriya da suka cancanci samun ilimi mai zurfi.

Masu ruwa da tsaki dai sun tabo batutuwan da suka shafi tsarin bayar da rancen kuɗin ga ɗalibai, musamman ma kan abin da ya shafi buƙatun cancanta, hanyoyin samar da kuɗaɗen, hanyoyin miƙa ɗalibai rancen da suka nema da kuma biyan bashin kuɗaɗen da sauran su.

Sabuwar dokar dai ita ce irinta ta farko a Najeriya a cewar Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Kasa, Femi Gbajabiamila.

Gbajabiamila wanda shi ne ya kawo kudurin dokar lokacin yana kakakin majalisa, ya ce dokar za ta inganta kasar domin babu wani yaron Najeriya da za a hana wa damar samun ilmi mai zurfi saboda rashin kuɗi.

Bello Wakili/Wababe

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai1 hour ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai2 hours ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Labarai15 hours ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai3 days ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Fasaha3 days ago

An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar

Kungiyar Malaman Jami’ar Jihar Sakkwato ASUU-SSU ta yi kira ga gwamnatin Jihar ta duba halin da kungiyar ke ciki da...

Kasuwanci3 days ago

Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

  Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin...

Ilimi3 days ago

Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark,...

Labarai6 days ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu. Jakadan...

Labarai1 week ago

Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar...

Mafi Shahara