Connect with us

Ilimi

An Haramta Fina-Finai Na Faɗan Daba Da Harkar Daudu A Kano

Published

on

Hukumar Tace Fina-Finai da Ɗab’i ta Kano ce ta ɗauki wannan mataki biyo bayan korafe-korafen da al’umma ke yi a kan shirya fina-finan da ke nuna faɗan daba da harkar daudu a jihar.

Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in yaɗa labarai na hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman ya fitar a Yammacin wannan Larabar.

Sanarwar ta ambato Shugaban Hukumar, Abba El-Mustapha ya ba da umarnin dakatarwa tare da hana dukkan fina-finan da ke nuna faɗan daba da harkar daudu a faɗin jihar jim kaɗan bayan wata ganawa da ya yi da manyan ma’aikatan hukumar.

Aminiya ta ruwaito cewa, ganawar Shugaban hukumar tace fina-finan ta haɗa da wasu daga cikin wakilan ’ya’yan masana’antar shirya fina-finan ta kannywood ciki har da kungiyoyin MOPPAN, Arewa Film Makers, Darektoci da Furodusoshi.

Abba El-Mustapha ya ce “doka ce ta ba wa hukumar damar dakatarwa ko hana duk wani fim da take ganin ya ci karo da tarbiya da al’adar al’ummar Kano.

“Saboda haka tuni lokaci ya shige da za a saka ido irin wannan gurbatattun fina-finai su ci gaba da yaduwa a cikin al’umma.

Abba El-Mustapha ya kuma gode wa ’yan masana’antar Kannywood dangane da haɗin kai da kuma goyan bayan da suke ba wa hukumar a koda yaushe.

“Ina kuma gode wa al’ummar Jihar Kano kan irin haɗin kan da suke ba wa Hukumar musamman wajen sanar da ita duk wani abu da suke ganin ya saba da al’ada da tarbiyar addinin musulunci.

Abba El-Mustapha ya kuma yi alkawarin ci gaba da barin kofarsa a buɗe domin karɓar shawarwari ga duk wanda suke da buƙatar hakan.

A ƙarshe ya ba wa masu shirya irin wannan fina-finai na faɗan daba ko harkar daudu damar wata ɗaya da su gyara ayyukansu kafin dokar ta fara aiki gadan-gadan a kansu.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai2 hours ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai2 days ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Fasaha3 days ago

An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar

Kungiyar Malaman Jami’ar Jihar Sakkwato ASUU-SSU ta yi kira ga gwamnatin Jihar ta duba halin da kungiyar ke ciki da...

Kasuwanci3 days ago

Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

  Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin...

Ilimi3 days ago

Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark,...

Labarai5 days ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Ilimi5 days ago

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu. Jakadan...

Labarai1 week ago

Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar...

Ilimi1 week ago

Daliban Jihar Kebbi Da Ke Kasashen Waje Za Su Sami Tallafin Naira Miliyan 309

Gwamnatin jihar Kebbi, ta amince da kashe sama da Naira miliyan Dari Uku da Tara, domin biyan tallafin karatu na...

Kasuwanci1 week ago

Kwari Masu Lalata Amfanin Gona Sun Mamaye Gonakin Tumatur A Kano

Shugaban kungiyar manoma ta jihar Kano, AFAN, Abdullahi Maibreadi, ya bukaci gwamnati a dukkan matakai da su taimaka wa manoma...

Mafi Shahara