Ilimi
Jami’ar Usman Danfodiyo Sokoto Za Ta Yaye Dalibai Dubu 23
Jami’ar Usman Danfodiyo Sokoto ta ce za ta yaye dalibai dubu ashirin da biyu da dari tara da talatin da biyu wadanda suka yi nasarar kammala karatunsu a fannoni daban-daban a Jami’ar.
Shugaban jami’ar Farfesa Lawal Suleiman Bilbis ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai da nufin fadakar da jama’a game da taron gangamin da aka shirya gudanarwa a ranar 15 ga watan Afrilun 2024 kuma ake sa ran kammala shi a ranar ashirin ga wannan wata.
Ya bayyana cewa bikin shi ne karo na 38, 39, 40 da kuma 41 na Jami’ar.
Farfesa Bilbis ya bayyana cewa, za a gabatar da wata lacca da mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro Malam Nuhu Rabado zai gabatar kan kalubalen rashin tsaro da ke addabar arewacin kasar, wanda aka shirya a ranar 18 ga watan Afrilu.
Shugaban jami’ar ya kara da cewa taron zai kuma bayar da lambar yabo ga wasu fitattun mahalarta taron.
NASIR MALALI/Wababe
-
Labarai3 days ago
Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa
-
Labarai6 days ago
Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano
-
Fasaha3 days ago
An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar
-
Kasuwanci3 days ago
Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno
-
Labarai13 hours ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa
-
Ilimi3 days ago
Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert