Connect with us

Fasaha

Sheikh Dahira Bauchi YA Sa Albarka Ga shirin Sa Ilimin Boko Ga Manhajar Makarantun Allo

Published

on

Fitaccen Malamin Addinin Musulunci a Bauchi Sheik Dahiru Usman Bauchi Ya Amince Da Hada Ilimin boko da Manhajin Almajiri.

 

Jagoran mabiya darikar Tijjaniya Sheikh Dahiru Usman Bauchi ya ce yana goyon bayan shirin gwamnatin tarayya na sanya ilimin boko a cikin manhajar karatun makarantun Almajiri.

 

Ya bayyana haka ne a lokacin da Babban Sakataren Hukumar Almajiri da Ilimin Yara marasa Makaranta ta kasa NCAOOSCE Dr Muhammad Sani Idris ya ziyarce shi a Bauchi.

 

Sheikh Dahiru Bauchi ya ce kungiyar Tijjaniya ta dukufa wajen ganin ta aiwatar da duk wani tsari da zai inganta zamantakewa da tattalin arzikin kasar nan.

 

Tun da farko Sakataren zartarwa na NCAOOSCE ya shaida wa Shehin Malamin cewa ya je gidansa ne domin neman albarkar sa yayin da ya fara ziyarce ziyarce don sake fasalin karatun Almajirai tare da kwashe miliyoyin yaran da ba sa zuwa makaranta a kan tituna.

 

Ya kuma jaddada cewa hadakar za ta baiwa almajirai damar samun ilimi da fasaha don yin gogayya a duniya.

 

Dr Muhammad Sani Idris ya kuma ce shugaban kasa Bola Tinubu ya damu da matsalar almajirai da yaran da ba su zuwa makaranta kuma ba zai bar wata kafa da za ta bi don kawo karshen ta ba.

Alhassan Bauchi/Wababe

Labarai

Labarai13 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar da Wutar Lantarki a Yankunan Kananan Hukumomin Jihar

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta gudanar da bikin bude tayin bada kwangilar samar da wutar lantarki a...

Labarai1 day ago

Shugaba Tinubu Ya Rantsar da Sabon Shugaban Hukumar Kidaya, Kwamishinoni da Manyan Sakatarori

Daga Bello Wakili Shugaba Bola Tinubu ya rantsar da Shugaban Hukumar Kidaya ta Kasa (NPC) da kwamishinoni biyu na hukumar,...

Labarai2 days ago

Rikicin Kungiyoyin Asiri Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Wani Matashi A Jihar Kwara

Daga Ali Muhammad Rabi’u An samu mummunan rikici tsakanin mambobin ƙungiyoyin asiri wanda ya shafi tsofaffin daliban kwalejin Kimiyya da...

Ilimi2 days ago

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Gurfanar da Iyayen Yaran da Ba Sa Zuwa Makaranta

Daga Aliyu Muraki Hukumar Ilimi Matakin Farko ta Jihar Nasarawa (NSUBEB) ta yi barazanar kamawa tare da gurfanar da iyayen...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Nada Janar Christopher Musa Sabon Ministan Tsaro

Daga Bello Wakili Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya nada Janar Christopher Gwabin Musa a matsayin sabon Ministan Tsaro. A...

Labarai3 days ago

Ministan Tsaro Badaru Abubakar Ya Yi Murabus

Daga Bello Wakili Ministan tsaron Najeriya, Alhaji Mohammed Badaru Abubakar, ya yi murabus daga mukaminsa nan take. Sanarwar da mai...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Jihar Kaduna Ta Gabatar Da Kasafin Kudin 2026 Na Kimanin Triliyan Daya

Daga Shamsuddeen Mannir Atiku  Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta karɓi daftarin kasafin kuɗin shekarar 2026 da ya zarce naira miliyan...

Labarai4 days ago

Najeriya Ta Kara Ƙaimi Wajen Kawar da Cutar HIV Nan da 2030

Daga Bello Wakili  Najeriya ta ƙarfafa ƙoƙarinta na kawar da cutar HIV nan da shekarar 2030, inda Uwargidar Shugaban Kasa,...

Labarai4 days ago

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Garin Eruka Na Jihar Kwara

Daga Ali Muhammad Rabi’u  ’Yan bindiga kimanin guda huɗu dauke da makamai sun kai hari a garin Eruku da ke...

Labarai4 days ago

Gwamnatin Kano Ta Kara Jaddada Dokar Haramcin Yin Haya da Babur a Jihar

Daga Abdullahi Jalaluddeen  Gwamnatin Jihar Kano ta sha alwashin daukar mataki kan masu yin haya da  babura a fadin jihar....

Mafi Shahara