Fasaha
Sheikh Dahira Bauchi YA Sa Albarka Ga shirin Sa Ilimin Boko Ga Manhajar Makarantun Allo
Fitaccen Malamin Addinin Musulunci a Bauchi Sheik Dahiru Usman Bauchi Ya Amince Da Hada Ilimin boko da Manhajin Almajiri.
Jagoran mabiya darikar Tijjaniya Sheikh Dahiru Usman Bauchi ya ce yana goyon bayan shirin gwamnatin tarayya na sanya ilimin boko a cikin manhajar karatun makarantun Almajiri.
Ya bayyana haka ne a lokacin da Babban Sakataren Hukumar Almajiri da Ilimin Yara marasa Makaranta ta kasa NCAOOSCE Dr Muhammad Sani Idris ya ziyarce shi a Bauchi.
Sheikh Dahiru Bauchi ya ce kungiyar Tijjaniya ta dukufa wajen ganin ta aiwatar da duk wani tsari da zai inganta zamantakewa da tattalin arzikin kasar nan.
Tun da farko Sakataren zartarwa na NCAOOSCE ya shaida wa Shehin Malamin cewa ya je gidansa ne domin neman albarkar sa yayin da ya fara ziyarce ziyarce don sake fasalin karatun Almajirai tare da kwashe miliyoyin yaran da ba sa zuwa makaranta a kan tituna.
Ya kuma jaddada cewa hadakar za ta baiwa almajirai damar samun ilimi da fasaha don yin gogayya a duniya.
Dr Muhammad Sani Idris ya kuma ce shugaban kasa Bola Tinubu ya damu da matsalar almajirai da yaran da ba su zuwa makaranta kuma ba zai bar wata kafa da za ta bi don kawo karshen ta ba.
Alhassan Bauchi/Wababe
-
Labarai3 days agoMinistan Tsaro Badaru Abubakar Ya Yi Murabus
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jihar Kaduna Ta Gabatar Da Kasafin Kudin 2026 Na Kimanin Triliyan Daya
-
Labarai4 days agoJihar Jigawa Ta Mayar da Rarar Kudi Sama da Naira Miliyan 50 Ga Maniyyatan Aikin Hajjin 2026
-
Labarai4 days ago‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Garin Eruka Na Jihar Kwara
-
Labarai4 days agoNajeriya Ta Kara Ƙaimi Wajen Kawar da Cutar HIV Nan da 2030
-
Labarai2 days agoShugaba Tinubu Ya Nada Janar Christopher Musa Sabon Ministan Tsaro
-
Labarai4 days agoGwamnatin Kano Ta Kara Jaddada Dokar Haramcin Yin Haya da Babur a Jihar
-
Labarai1 day agoShugaba Tinubu Ya Rantsar da Sabon Shugaban Hukumar Kidaya, Kwamishinoni da Manyan Sakatarori
