Connect with us

Ilimi

Farfesa Gumel Ya Fitar da Sabon Tsari da Zai Daga Martabar FUD

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria 

Sabon Shugaban Jami’ar Tarayya ta Dutse (FUD), Farfesa Ahmad Mohammed Gumel, ya bayyana cikakken shiri da zai sauya jami’ar zuwa cibiyar bincike, kirkire-kirkire da kuma ingantaccen ilimi a Najeriya nan da shekarar 2030.

Farfesa Ahmad Gumel ya bayyana hakan ne yayin da yake gabatar da manufofinsa lokacin da ya karɓi ragamar aiki a hukumance a matsayin Shugaban jami’ar na huɗu.

Ya jaddada muhimmancin samar da ɗaliban da ke da ƙwarewa, nagarta da kuma bayar da gudunmawa mai ma’ana ga ci gaban ƙasa.

A cewarsa, wannan shirin sauyi yana tafiya ne bisa wani tsarin bunƙasa jami’a mai manufofin goma sha ɗaya, inda aka fi bai wa fannonin inganta ilimi, bincike da kirkire-kirkire, bunƙasa fasahar zamani, da inganta jin daɗin ɗalibai da ma’aikata muhimmanci.

Ya bayyana cewa jami’ar za ta sabunta tsarin karatunta domin ya dace da ƙa’idojin Hukumar Jami’o’i ta Ƙasa (NUC) da kuma kyawawan ƙa’idojin ilimi na duniya, tare da shirin ƙaddamar da sabbin shirye-shiryen karatu kamar Fasahar Basirar Na’ura (Artificial Intelligence), Kimiyyar Bayanai (Data Science), Cloud Computing, Noman da ya dace da sauyin yanayi (Climate-Smart Agriculture), da sauran sabbin fannoni.

Shugaban jami’ar ta FUD ya tabbatar wa masu ruwa da tsaki cewa an tsara cikakken shirin bunƙasa jami’ar na shekaru biyar, wanda nan ba da jimawa ba za a gabatar da shi ga majalisar gudanarwa domin amincewa.

Labarai

Labarai18 hours ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai2 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Ilimi2 days ago

Hukumar Ilimantar Da Makiyaya Ta Kasa Ta Horarda Ma’aikatanta Kan Yanda Za’a Mayarda ‘Ya’yan Makiyaya Makaranta 

  By Adamu Yusuf   Hukumar Ilimantar da Makiyaya Ta Kasa (NCNE) ta shirya taron horas da ma’aikatan ta kan...

Labarai2 days ago

NCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji

Daga Sani Dutsinma Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya (NCAA), ta yaba da kokarin Hukumar Jin Daɗin Alhazai...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina

Rundunar sojin Najeriya ta kashe ’yan bindiga 45 a wani mummunan artabu da aka yi a yankin Danmusa na cikin...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya

Gwamnatin Jihar Kebbi ta karyata zargin cewa gwamnatin Gwamna Nasir Idris ba ta taka rawar gani wajen bunkasa harkokin addinin...

Labarai2 days ago

Ranar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata

Kwamishinar Harkokin Mata, Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Amina Abdullahi, ta bukaci masu ruwa da tsaki...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yi Kira Da A Karfafa Mata

Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta bukaci hukumomin gwamnati, abokan hulda na ci gaba, sarakuna, malamai da...

Labarai2 days ago

’Yan Sanda Sun Kama Mutane Biyu Kan Lalata Kayan Wutar Lantarki a Nasarawa

Rundunar ’yan sandan Jihar Nasarawa ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da lalata igiyoyi da sandunan wutar lantarki...

Labarai2 days ago

NSCDC Ta Kama Mutane Biyu Da Ake Zargin ’Yan Bindiga Ne a Kwara

Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya NSCDC a Jihar Kwara ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da alaka...

Mafi Shahara