Ilimi
Farfesa Tukur Adamu Ya Fara Aiki a Matsayin Shugaban Jami’ar Tarayya Gusau na Hudu
Daga Aminu Dalhatu
Sabon Shugaban Jami’ar Tarayya ta Gusau (FUGUS) Farfesa Tukur Adamu ya yi alƙawarin inganta ilimi, bincike, ƙirƙire-ƙirƙire, walwalar ɗalibai da ma’aikata.
Farfesa Tukur Adamu wanda ya gaji Professor Mu’azu Gusau Abubakar bayan kammala wa’adinsa na shekaru biyar, ya bayyana hakan ne yayin da ya karɓi ragamar shugabancin Jami’ar a matsayin shugabata na huɗu.
Sabon Shugaban ya ce zai mayar da hankali kan binciken da zai magance matsalolin al’umma, kamar yadda ya yi a UDUS.
Ya kuma yi alƙawarin haɗa kai da gwamnatin Zamfara, Sarakuna, Jami’an tsaro da ƙungiyoyin addini domin ci gaban jami’ar.
An naɗa shi ne a taron Majalisar Gudanarwar jami’ar a watan Disamba 2025.
-
Labarai6 days agoRamadan: Sarkin Kauru Ya Bukaci a Kara Karfafa Tsaro Tare da Tallafawa Marasa Galihu
-
Labarai5 days agoKaramar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro
-
Labarai5 days agoSojojin Najeriya Sun Karɓi Motocin Yakin Da Aka Kera A Cikin Ƙasa
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam
-
Labarai2 days agoRanar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata
-
Labarai5 days agoTsarin Kundin Shirin Bunkasa Samarda Abinci Mai Gina Jiki
-
Labarai6 days agoKungiyoyin Alumma a Jigawa Sun Bayyana Goyon Bayansu ga Gwamna Namadi Kan Lamarin Walida Abdulhadi
-
Labarai4 days agoGwamnatin Zamfara Ta Ayana Dokar Ta-baci Kan Shan-Inna a Karamar Hukumar Gummi
