Connect with us

Kasuwanci

Gwamnan Jigawa Namadi Na Jagorantar Ziyarar Nazarin Noman Alkama a Habasha

Published

on

 

Gwamnan jihar Umar Namadi ya fara wani gagarumin ziyarar gani da ido zuwa kasar Habasha tare da wata babbar tawaga da ta hada da manyan mataimaka a harkokin noma, jami’ai, da kwararru daga ma’aikatar noma ta jihar da hukumomin da abin ya shafa.

 

A cikin wata sanarwa da babban sakataren yada labarai na gwamnan Hamisu Mohammed Gumel ya raba wa gidan rediyon Najeriya ya bayyana cewa, makasudin ziyarar shi ne nazarin shirin noman alkama na kasar Habasha da kuma gudanar da wani cikakken shiri da manufar dawowa gida sabbin dabaru da kwarewa zuwa gida

 

A cewarsa, alkama, kasancewarta ta biyu mafi girman abin bukata a duniya, tana da matukar muhimmanci wajen magance kalubalen samar da abinci a duniya.

 

Ya ce, a bisa wannan yanayin, Habasha ta zama babbar jigo a fannin noman alkama a Afirka, wanda ya nuna gagarumar nasarar da aka samu wajen dorewar noma da samar da albarkatu.

 

Hamisu Mohammed Gumel ya ci gaba da bayyana cewa, ziyarar na da manufar cimma muhimman manufofi da suka hada da tantance shirin noman alkama na kasar Habasha da kuma fa’idarsa.

 

Ya yi nuni da cewa, sauran muradun sun hada da samar da hanyoyin yin musanyar ilimi kan tsarin noman alkama, da magance kalubalen da ake fuskanta wajen samar da alkama mai dorewa, da inganta hadin gwiwa tsakanin Habasha da Najeriya wajen daukar sabbin dabarun noma.

 

Ya bayyana cewa musamman wuraren da aka fi mayar da hankali a kai sun hada da fahimtar tsare-tsare na dogon lokaci na Habasha na noman alkama, da tantance ci gaban da aka samu da kalubale, da binciko hanyoyin samar da kayayyaki daban-daban, da kuma baje kolin ingantattun samfura kamar noma kasuwanci.

 

Ya ce, a ziyarar aiki ta kwanaki hudu, tawagar ta Jigawa, da wasu muhimman abubuwa, za su dauki darussa kan noman ruwan sama da noman alkama na ban ruwa a jihohi daban-daban na kasar Habasha, da kuma samun nasarar samar da alkama mai dorewa.

 

Hakama yayi nuni da cewa, jihar Jigawa a halin yanzu ita ce kan gaba wajen noman alkama a Najeriya, wanda ke bayar da gudunmawa sosai a fannin noma da samar da abinci, kuma ana sa ran rangadin binciken zai bude wa jihar damammaki tare da cimma wasu muhimman sakamako da za su taimaka wajen bunkasa noman alkama mai dorewa a jihar.

 

Gumel ya kara da cewa, ziyarar ta jaddada kudirin gwamnatin Gwamna Umar Namadi a jihar na binciko sabbin hanyoyin noma domin inganta samar da abinci da kuma mayar da harkar noma sana’ar kasuwanci ga al’ummar jihar da galibin masu noma ne.

USMAN MZ?Wababe

Labarai

Labarai19 hours ago

Iran Da Amurka Za Su Ci Gaba Da Tattaunawa Kan Shirin Nukiliyar Tehran

Iran da Amurka za su shiga zagaye na biyu na tattauna batun taƙaita shirin nukiliyar Tehran a yau Asabar. Masu...

Labarai19 hours ago

Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Zargin Takurawa Mataimakin Shugaban Kasa Shettima

Fadar shugaban kasa ta musanta rahotannin da ke nuni da cewa an hana mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, GCON shiga...

Kasuwanci19 hours ago

‘Yan Sandan Sun Ceto Wasu Mutane Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Zamfara

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta yi nasarar kubutar da wasu mutane shida da aka yi garkuwa da su, a...

Kasuwanci20 hours ago

Gwamna Abdulrazaq Ya Bukaci Kiristoci Da Su Tuna Da Darussan Lokacin Ista

Gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya bukaci Kiristoci da su yi tunani a kan darussa, muhimmaci, da kuma kyawawan dabi’u...

Kasuwanci20 hours ago

Shugaban Majalisar Neja Ya Mika Sakon Easter Ga Al’ummar Kirista.

Kakakin majalisar dokokin jihar Neja, Barr. Abdulmalik Sarkin-Daji, ya mika sakon taya murna ga al’ummar kiristoci a jihar da ma...

Kasuwanci20 hours ago

Rundunar ‘Yansan Nijeriya Za Ta Gudanar Atisaye Ga Jami’anta a Jigawa

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta sanar da cewa za ta gudanar da atisayen harbe-harbe ga sabbin ‘yan sanda a karamar...

Labarai20 hours ago

Sarakuna Suna Bada Gudunmuwa Wajen Samarda Lafiya Da Hadin Kan Kasa– Kungiyar Sarakunan Afirka

    Kungiyar Sarakunan Afirka ta jaddada muhimmancin gudunmuwar da Sarakuna ke badawa wajen tabbatar da hadin kai da zaman...

Labarai1 day ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Ya Yi Bikin Easter Tare da Al’ummomin Kiristoci

  Makera, Jihar Kaduna – Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, Rt. Hon. Yusuf Dahiru Liman, ya halarci bukukuwan Easter tare...

Fasaha2 days ago

Gwamnatin Trayya Zata Zamantar da Kayayyakin Watsa Labaran ta

Gwamnatin tarayya ta jaddada kudirinta na kawo sauyi da kuma zamanantar da kafafen yada labarai na Najeriya da watsa shirye-shirye...

Kasuwanci2 days ago

Hukumar NSCDC ta tura jami’an tsaro 415 domin aikin Easter a Zamfara.

Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya (NSCDC) reshen jihar Zamfara, ta tura jami’ai 415 a fadin jihar domin tabbatar da...

Mafi Shahara