Connect with us

Kasuwanci

Gwamnan Jigawa Namadi Na Jagorantar Ziyarar Nazarin Noman Alkama a Habasha

Published

on

 

Gwamnan jihar Umar Namadi ya fara wani gagarumin ziyarar gani da ido zuwa kasar Habasha tare da wata babbar tawaga da ta hada da manyan mataimaka a harkokin noma, jami’ai, da kwararru daga ma’aikatar noma ta jihar da hukumomin da abin ya shafa.

 

A cikin wata sanarwa da babban sakataren yada labarai na gwamnan Hamisu Mohammed Gumel ya raba wa gidan rediyon Najeriya ya bayyana cewa, makasudin ziyarar shi ne nazarin shirin noman alkama na kasar Habasha da kuma gudanar da wani cikakken shiri da manufar dawowa gida sabbin dabaru da kwarewa zuwa gida

 

A cewarsa, alkama, kasancewarta ta biyu mafi girman abin bukata a duniya, tana da matukar muhimmanci wajen magance kalubalen samar da abinci a duniya.

 

Ya ce, a bisa wannan yanayin, Habasha ta zama babbar jigo a fannin noman alkama a Afirka, wanda ya nuna gagarumar nasarar da aka samu wajen dorewar noma da samar da albarkatu.

 

Hamisu Mohammed Gumel ya ci gaba da bayyana cewa, ziyarar na da manufar cimma muhimman manufofi da suka hada da tantance shirin noman alkama na kasar Habasha da kuma fa’idarsa.

 

Ya yi nuni da cewa, sauran muradun sun hada da samar da hanyoyin yin musanyar ilimi kan tsarin noman alkama, da magance kalubalen da ake fuskanta wajen samar da alkama mai dorewa, da inganta hadin gwiwa tsakanin Habasha da Najeriya wajen daukar sabbin dabarun noma.

 

Ya bayyana cewa musamman wuraren da aka fi mayar da hankali a kai sun hada da fahimtar tsare-tsare na dogon lokaci na Habasha na noman alkama, da tantance ci gaban da aka samu da kalubale, da binciko hanyoyin samar da kayayyaki daban-daban, da kuma baje kolin ingantattun samfura kamar noma kasuwanci.

 

Ya ce, a ziyarar aiki ta kwanaki hudu, tawagar ta Jigawa, da wasu muhimman abubuwa, za su dauki darussa kan noman ruwan sama da noman alkama na ban ruwa a jihohi daban-daban na kasar Habasha, da kuma samun nasarar samar da alkama mai dorewa.

 

Hakama yayi nuni da cewa, jihar Jigawa a halin yanzu ita ce kan gaba wajen noman alkama a Najeriya, wanda ke bayar da gudunmawa sosai a fannin noma da samar da abinci, kuma ana sa ran rangadin binciken zai bude wa jihar damammaki tare da cimma wasu muhimman sakamako da za su taimaka wajen bunkasa noman alkama mai dorewa a jihar.

 

Gumel ya kara da cewa, ziyarar ta jaddada kudirin gwamnatin Gwamna Umar Namadi a jihar na binciko sabbin hanyoyin noma domin inganta samar da abinci da kuma mayar da harkar noma sana’ar kasuwanci ga al’ummar jihar da galibin masu noma ne.

USMAN MZ?Wababe

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai8 hours ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai3 days ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Fasaha3 days ago

An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar

Kungiyar Malaman Jami’ar Jihar Sakkwato ASUU-SSU ta yi kira ga gwamnatin Jihar ta duba halin da kungiyar ke ciki da...

Kasuwanci3 days ago

Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

  Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin...

Ilimi3 days ago

Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark,...

Labarai6 days ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu. Jakadan...

Labarai1 week ago

Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar...

Ilimi1 week ago

Daliban Jihar Kebbi Da Ke Kasashen Waje Za Su Sami Tallafin Naira Miliyan 309

Gwamnatin jihar Kebbi, ta amince da kashe sama da Naira miliyan Dari Uku da Tara, domin biyan tallafin karatu na...

Kasuwanci1 week ago

Kwari Masu Lalata Amfanin Gona Sun Mamaye Gonakin Tumatur A Kano

Shugaban kungiyar manoma ta jihar Kano, AFAN, Abdullahi Maibreadi, ya bukaci gwamnati a dukkan matakai da su taimaka wa manoma...

Mafi Shahara