Labarai
Sojojin Nijeriya Sun Kubutarda Mutane 16 a Kajuru
Sojojin Najeriya ƙarƙashin runduna ta ɗaya sun kuɓutar da mutum 16 da ƴanbindiga suka sace a yankin Kajuru da ke jihar Kaduna.
Sun kuma daƙile yunƙurin wata ƙungiyar miyagu na yin garkuwa da mutane.
Cikin wata sanarwa da daraktan yaɗa labarai na rundunar sojin, Manjo Janar Onyema Nwachukwu ya fitar, rundunar ta ce sojojin da aka tura ƙarƙashin runduna ta ɗaya sun daƙile yunƙurin sace mutane tare da ceto mutanen da aka sace a yankin Tantatu da ke ƙaramar hukumar Kajuru a jihar Kaduna.
A cewar sanarwar, sojojin sun kai samamen ne bayan bayanan sirrin da suka samu ranar Lahadi da daddare lokacin da suka bi sawun ƴanbindigar da suka sace wasu mutane a ƙauyen.
“Da isar su wajen da lamarin ya faru, sojoji sun bi ƴanbindigar, inda suka yi musayar wuta daga bisani kuma suka kuɓutar da mutum 16 da aka sace,” in ji sanarwar.
“Sojojin na ci gaba da gudanar da bincike a cikin dazuka domin ganowa tare da tseratar da sauran mutanen da aka yi garkuwa da su tare da murƙushe miyagun ayyukan ƴanbindigar.”S
hugaban hafsan sojojin ƙasa Taoreed Lagbaja ya yaba wa sojojin kan ƙoƙarin nasu tare da neman su ƙara ƙaimi wajen fatattakar masu aikata ta’addanci.
-
Labarai1 day ago
NAHCON Ta Jinjinawa Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Bisa Shirye-shiryen Hajjin Bana
-
Labarai1 day ago
Amurka Ta Dakatar Da Kudurin Kai Jirgin Bama-Bamai Zuwa Isra’ila
-
Ilimi5 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura
-
Labarai6 days ago
An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya
-
Fasaha2 days ago
Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno
-
Kasuwanci2 days ago
CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati
-
Fasaha2 days ago
Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet
-
Labarai2 hours ago
Kotu ta Bayar da Belin Hadi Sirika kan Naira Miliyan 100