Labarai
Kotu ta Bayar da Belin Hadi Sirika kan Naira Miliyan 100
Tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama na Nijeriya, Hadi Sirika ya musanta zargin aikata laifin almundahana da ya shafi kusan Naira biliyan 2.7 da Gwamnatin Tarayya ta shigar da ƙara a kansa.
An gurfanar da Sirika ne a gaban mai shari’a Sylvanus Oriji Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja a ranar Alhamis tare da ‘yarsa Fatima, da sirikinsa, Jalal Sule Hamma, da wani kamfani mai suna Al Buraq Global Investment Limited.
A ranar Larabar da ta gabata ne Hukumar Yaƙi da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) ta ce za ta gurfanar da Sirika da wasu mutane uku a gaban kuliya.
Takardar tuhumar ta yi zargin cewa Sirika ya yi amfani da mukaminsa na minista wajen bayar da kwangila ga ‘yarsa da surukinsa, da kuma abokan huldarsa.
Ita ma ‘yar tasa da surukin nasa da suka halarci kotun tare sun musanta zargin da ake musu na tuhuma shida da aka karanta musu, kamar yadda kafar watsa labarai ta Channels ta rawaito. Bayan musanta tuhumar da ake yi musu ta zamba, lauyoyinsu sun gabatar da bukatar neman belinsu wanda alkali ya bayar.
-
Labarai5 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha6 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai4 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai6 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai6 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar
-
Labarai6 days ago
Varane zai bar Manchester United