Connect with us

Labarai

Tsananin Zafin Rana Tsakanin Kasashen Africa

Published

on

 

Sudan ta Kudu da Kenya da Senegal da Mali sun fitar da sanarwar gargaɗi kan matsanancin zafi yayin da yanayin zafin da aka alaƙanta da ɗumamar yanayi ya bazu a yankunan Afirka.

Sudan ta Kudu ta rufe makarantu domin kare yara yayin da ake sa ran yanayin zai kasi maki 45 a ma\aunin salshiyos.

A Kenya, hukumar kula da yanayi a ƙasar ta gargaɗi yankunan da ke arewaci kan cewa za su fuskanci matsalar zafi da ta zarce digiri 30 kan ma’aunin salshiyos daga yau zuwa kwanaki 10 masu zuwa.

An samu irin wannan yanayi na zafi a Senegal inda aka yi fama da matsanancin zafin na tsawon kwanaki a faɗin ƙasar kamar yadda kafar yaɗa labarai ta Dakaractu ta ruwaito.

Hukumar kula da yanayi ta Senegal ta ce yanayin zai kai tsakanin digiri 44 da 45 a kan ma’aunin salshiyos musamman a yankin kudu maso gabashin ƙasar. Yayin da yankin tsakiya da kudu maso yamma za su kasance cikin yanayin zafin da ya haura maki 42 a ma’aunin salshiyos.

A Mali ma, tsakiyar Bankass Circle da ke yankin Mopti ta sake nazarin jadawalin karatun makarantu a yanayin zafin, in ji kafar yaɗa labarai mai zaman kanta, Studio Tamani.

Matsanancin zafin a gabashin Afirka dai an alaƙanta shi da yanayin El Nino da ke yawan faruwa idan koguna suka yi zafi kuma suka gangaro kan ƙasa a gaɓar ruwan Amurka ta kudu kuma ya afka cikin koguna.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai20 hours ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Ilimi22 hours ago

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu. Jakadan...

Labarai3 days ago

Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar...

Ilimi3 days ago

Daliban Jihar Kebbi Da Ke Kasashen Waje Za Su Sami Tallafin Naira Miliyan 309

Gwamnatin jihar Kebbi, ta amince da kashe sama da Naira miliyan Dari Uku da Tara, domin biyan tallafin karatu na...

Kasuwanci3 days ago

Kwari Masu Lalata Amfanin Gona Sun Mamaye Gonakin Tumatur A Kano

Shugaban kungiyar manoma ta jihar Kano, AFAN, Abdullahi Maibreadi, ya bukaci gwamnati a dukkan matakai da su taimaka wa manoma...

Fasaha3 days ago

Shugaba Tinubu Ya Kaddamar Shirin Bada Bashin Kayyaki Ga ‘Yan Kasa

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya ƙaddamar da kashin farko na tsarin karɓar bashin kaya ga ƴan ƙasar. Bayanin hakan na...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Jihar Kaduna Ta Rufe Bankin UBA Kan Kin Biyan Haraji

Hukumar Tara Kudaden Haraji ta Jihar Kaduna (KADIRS) ta raufe rassan bankin UBA kan kin biyan harajin Naira miliyan 14....

Labarai4 days ago

Mutum Biyar Sun Mutu Cikin Kwale-Kwalen ƴan Ci-Rani

Mutum biyar har da yaro sun mutu yayin da suke ƙoƙarin tsallake hanyar ruwa da ta ratsa Ingila da safiyar...

Kasuwanci4 days ago

CBN Ya Sake Karya Farashin Dala Zuwa N1,101

Babban Bankin Nigeria CBN ya sake sanar da matakin karya farashin dala daga N1,251 zuwa N1,101. CBN ya bayyana haka...

Ilimi4 days ago

Ƴan Sanda Za Su Yi Bincike Kan Makarantar Leads British

Rundunar ƴan sanda a babban birnin tarayya Abuja ta ce ta aika tawagar jami’anta zuwa makarantar Leads British bayan bidiyon...

Mafi Shahara