Labarai
Tsananin Zafin Rana Tsakanin Kasashen Africa
Sudan ta Kudu da Kenya da Senegal da Mali sun fitar da sanarwar gargaɗi kan matsanancin zafi yayin da yanayin zafin da aka alaƙanta da ɗumamar yanayi ya bazu a yankunan Afirka.
Sudan ta Kudu ta rufe makarantu domin kare yara yayin da ake sa ran yanayin zai kasi maki 45 a ma\aunin salshiyos.
A Kenya, hukumar kula da yanayi a ƙasar ta gargaɗi yankunan da ke arewaci kan cewa za su fuskanci matsalar zafi da ta zarce digiri 30 kan ma’aunin salshiyos daga yau zuwa kwanaki 10 masu zuwa.
An samu irin wannan yanayi na zafi a Senegal inda aka yi fama da matsanancin zafin na tsawon kwanaki a faɗin ƙasar kamar yadda kafar yaɗa labarai ta Dakaractu ta ruwaito.
Hukumar kula da yanayi ta Senegal ta ce yanayin zai kai tsakanin digiri 44 da 45 a kan ma’aunin salshiyos musamman a yankin kudu maso gabashin ƙasar. Yayin da yankin tsakiya da kudu maso yamma za su kasance cikin yanayin zafin da ya haura maki 42 a ma’aunin salshiyos.
A Mali ma, tsakiyar Bankass Circle da ke yankin Mopti ta sake nazarin jadawalin karatun makarantu a yanayin zafin, in ji kafar yaɗa labarai mai zaman kanta, Studio Tamani.
Matsanancin zafin a gabashin Afirka dai an alaƙanta shi da yanayin El Nino da ke yawan faruwa idan koguna suka yi zafi kuma suka gangaro kan ƙasa a gaɓar ruwan Amurka ta kudu kuma ya afka cikin koguna.
-
Labarai3 days ago
Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai
-
Kasuwanci4 days ago
CBN Ya Sake Karya Farashin Dala Zuwa N1,101
-
Fasaha3 days ago
Shugaba Tinubu Ya Kaddamar Shirin Bada Bashin Kayyaki Ga ‘Yan Kasa
-
Labarai20 hours ago
Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano
-
Labarai5 days ago
An Kwashe Mutane Da Dama Bayan Mummunar Ambaliyar A China
-
Fasaha5 days ago
Mutane 3 Sun Mutu a Salga a Kano
-
Labarai5 days ago
Shugaban Hukumar Leken Asirin Isra’ila Ya Yi Murabus
-
Kasuwanci4 days ago
Gwamnatin Jihar Kwara Ta Dakatar Da Yanka Nama A Mahauta Na Kwanaki 3