Connect with us

Labarai

Mutum Biyar Sun Mutu Cikin Kwale-Kwalen ƴan Ci-Rani

Published

on

Mutum biyar har da yaro sun mutu yayin da suke ƙoƙarin tsallake hanyar ruwa da ta ratsa Ingila da safiyar ranar Talata, in ji hukumomin Faransa.

Masu gadin teku sun ce mutanen da lamarin ya rutsa da su na koƙarin zuwa Birtaniya ne cikin wani kwale-kwale maƙare da ƴan ci-rani 110.

Tuni aka ƙaddamar da aikin ceto domin zaƙulo mutanen da suke cikin ruwa.

Sakataren harkokin cikin gida na Birtnaiyam James Cleverly ya ce: “Dole ne a magance wannan bala’i. Ba zan amince da halin da ake ciki ba da ke janyo asarar rayuka.”

Mista Cleverly ya ce gwamnatin Birtaniya tana yin duk mai yiwuwa na kawo ƙarshen miyagu masu safarar mutane.”

Tun farko, majalisar dokokin Birtaniya ta amince da ƙudirin neman tura masu neman mafaka a Birtaniya zuwa Rwanda bayan shafe watanni ana ƙiƙi-ƙaƙa a kai.

Kudurin ya ayyana Rwanda a matsayin kasar da ba ta da wata matsala dangane da ƙudurin, bayan da kotun ƙolin Birtaniya ta zartar a watan Nuwamba cewa shirin na gwamnati ya saba doka.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Ilimi2 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta ci gaba da tallafawa harkokin koyo da koyarwa a Jami’ar Fasaha ta Gwamnatin...

Labarai2 days ago

An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya

Shugaban kungiyar masu noman rogo ta Najeriya (NCGA), Mustapha Othman Bakano, ya kaddamar da wani tsari na samar da kasuwa...

Labarai4 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai4 days ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Labarai4 days ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai6 days ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Fasaha7 days ago

An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar

Kungiyar Malaman Jami’ar Jihar Sakkwato ASUU-SSU ta yi kira ga gwamnatin Jihar ta duba halin da kungiyar ke ciki da...

Kasuwanci7 days ago

Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

  Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin...

Ilimi7 days ago

Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark,...

Labarai1 week ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Mafi Shahara