Labarai
An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya
Shugaban kungiyar masu noman rogo ta Najeriya (NCGA), Mustapha Othman Bakano, ya kaddamar da wani tsari na samar da kasuwa mai kyau da nufin karfafa wa manoman rogo da bunkasa harkar noma a Najeriya.
Alhaji Mustapha Othman Bakano ya bayyana bukatar samar da ingantattun hanyoyin kasuwanci don saukaka fitar da rogo kasuwannin ketare da kuma samar da kudaden musaya ga kasa.
Ya ce kungiyar na baiwa manoman da suka yi rajista da ita damar baje kolin kayayyakin amfanin gona da kuma cudanya da masu zuba jari na kasashen waje ba tare da wata matsala ba.
A karkashin sabon tsarin, Mustapha Bakano ya bayyana shirin samar da masana’antun sarrafa rogo a kowane yanki domin saukaka ayyuka da kuma bunkasa kasuwa ga manoma.
Baya ga samun kasuwa, shugaban kungiyar ya bayyana kokarin da ake yi na inganta dabarun noman rogo da rage lokacin girbi.
A cewarsa, ta hanyar bincike da ayyukan ci gaba, NCGA na kokarin inganta noman rogo domin wadata kasa da abinci.
Mustapha Bakano ya kara da cewa kungiyar za ta samar da dabarun kare manoma daga barazanar tsaro, inda za ta yi hadin gwiwa da jami’an tsaro domin kare lafiyarsu da kuma amfanin gona.
Hajazalika ya ce kungiyar za ta yi amfani da fasahar zamani wajen kare manoma daga fuskantar duk wata barazana ga amfanin gonarsu.
Ya ce a yanzu ya mayar da hankali ne wajen ganin an magance matsalar karancin abinci a jihar Kaduna da ma kasa baki daya, yana mai cewa zai kara jajircewa wajen yin amfani da kwarewarsa domin samar da ci gaba mai dorewa a fannin noma a Najeriya.
Umar S Fada
-
Labarai3 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi5 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha5 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai4 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai4 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai2 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai4 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai4 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar