Connect with us

Labarai

An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya

Published

on

Shugaban kungiyar masu noman rogo ta Najeriya (NCGA), Mustapha Othman Bakano, ya kaddamar da wani tsari na samar da kasuwa mai kyau da nufin karfafa wa manoman rogo da bunkasa harkar noma a Najeriya.

 

Alhaji Mustapha Othman Bakano ya bayyana bukatar samar da ingantattun hanyoyin kasuwanci don saukaka fitar da rogo kasuwannin ketare da kuma samar da kudaden musaya ga kasa.

 

Ya  ce kungiyar na  baiwa  manoman da suka yi rajista da ita  damar baje kolin kayayyakin amfanin gona da kuma cudanya da masu zuba jari na kasashen waje ba tare da wata matsala ba.

 

A karkashin sabon tsarin, Mustapha Bakano ya bayyana shirin samar da masana’antun sarrafa rogo a kowane yanki domin saukaka ayyuka da kuma bunkasa kasuwa ga manoma.

 

Baya ga samun kasuwa, shugaban kungiyar ya bayyana kokarin da ake yi na inganta dabarun noman rogo da rage lokacin girbi.

 

A cewarsa, ta hanyar bincike da ayyukan ci gaba, NCGA na kokarin inganta noman rogo domin wadata kasa da abinci.

 

Mustapha Bakano ya kara da cewa kungiyar za ta samar da dabarun kare  manoma daga barazanar tsaro,  inda za ta yi hadin gwiwa da jami’an tsaro domin kare lafiyarsu da kuma  amfanin gona.

 

Hajazalika ya ce kungiyar za ta yi amfani da fasahar zamani wajen kare manoma daga fuskantar duk wata barazana ga amfanin gonarsu.

 

Ya ce a yanzu ya mayar da hankali ne wajen ganin an magance matsalar karancin abinci a jihar Kaduna da ma kasa baki daya, yana mai cewa zai kara jajircewa wajen yin amfani da kwarewarsa domin samar da ci gaba mai dorewa a fannin noma a Najeriya.

 

Umar S Fada

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai2 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai2 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai2 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi2 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai3 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai3 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai4 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai4 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai4 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai4 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara