Connect with us

Ilimi

Mutane fiye da dubu 200 muka ba taimakon Lauya – Barista Aliyu

Published

on

 

An bayyana bukatar sake nazarin tsarin shari’ar kasan nan muddun ana bukatar rage cinkoson da ake da shi a gidajen gyaran hali da ke fadin kasan nan

Gwamnan Jihar Plateau Caleb Muftwang ya bayyana haka lokacin da kungiyar bada tallafin aikin lauya ta kasa ta ziyarce shi a gidan gwamnati

Ita dai wannan kungiyar da ke bada agajin aikin lauya ga marasa karfj da ake tuhuma da aikata wani laifi ta zamo gatan marasa gata a kasan nan.

Don tabbatar da wannan kirarin da ake yiwa kungiyar, ta ziyarci dukkanin gidajen gyaran hali da ke kasan nan domin tabbatar da ta tallafawa wadanda ke tsare ba su da karfin daukar lauyan da zai Kare su.

Gwamnan jihar Plateau ya fadawa masu ziyarar cewa, saboda rashin adalci da daidaito ya sa ake samun aikata laifuka, don haka yace akwai bukatar yiwa tsarin shari’ar kasan nan gyaran fuska don maganin wannan matsala.

 

Gwamnan Wanda ya bayyana takaicin sa ganin yadda ake samun cinkoso a gidajen gyaran Hali da ke kasan Nan, yace ana shirin samarda Karin gidan gyaran Hali a Jos ta Gabas.

 

Tunda farko shugaban masu ziyarar kuma shugaban kungiyar Barista Aliyu Abubakar yace kungiyar su ta nada agajin lauya ga mutane fiye da dubu 200 daga shekara ta 2021 zuwa bara 2023, don yayi Kiran samun goyon baya ga kungiyar domin su ci gaba da aikin su.

 

Yace manufar kungiyar su, ita ce su samarda wata kasa da za a ce an Sami daidaita tsakanin dukkanin ‘yan kasa

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Kasuwanci22 hours ago

CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati

Babban Bankin Najeriya CBN ya bayar da wa’adin ranar 7 ga watan  Yulin 2024 ga masu POS su kammala rajista...

Fasaha1 day ago

Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno

  Gwamnatin jihar Borno ta fara aikin horas da malamai 1,949 a matakin farko da aka gano cewa suna iya...

Fasaha1 day ago

Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet

  Babban Bankin Najeriya (CBN) ya umurci bankunan kasar su fara cirar kaso 0.5 cikin 100 na duk kuɗin da...

Labarai1 day ago

An kashe Falasɗinawa 34,800 tun fara yaƙi – Ma’aikatar lafiyar Hamas

Ma’aikatar lafiya ta Hamas a Gaza ta ce an kashe Falasdinawa 34,789 a yankin tun ranar 7 ga watan Oktoba,...

Ilimi4 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta ci gaba da tallafawa harkokin koyo da koyarwa a Jami’ar Fasaha ta Gwamnatin...

Labarai5 days ago

An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya

Shugaban kungiyar masu noman rogo ta Najeriya (NCGA), Mustapha Othman Bakano, ya kaddamar da wani tsari na samar da kasuwa...

Labarai6 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai6 days ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Labarai7 days ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai1 week ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Mafi Shahara