Labarai
Gwamnatin Kano Ta Raba Kayan Abinci Ga Majinyata A Asibitoci
Gwamnatin jihar Kano ta kaddamar da rabon kayan abinci ga marasa lafiya da ke kwance a asibitocin gwamnati dake fadin jihar.
Kwamishinan Yada Labarai na Jihar Kano, Baba Halilu Dantiye, wanda ya jagoranci rabon kayayyakin da suka hada buhun shinkafa mai nauyin kilogiram 19 da na masara kilogiram 10 ga majinyata a Asibitin da ake kula da cututtuka masu yaduna da na Abubakar Imam a madadin Gwamnan, ya ce an gudanar da shirin ne da nufin bada tallafiwa marasa karfi.
Ya bayyana cewa an raba buhunan shinkafa da masara dubu hudu da dari huda da ashirin da shidda ga majinyatan da ke kwance a manyan da kananan asibitoci.
Kwamishinan ya bayyana cewa gwamnatin Gwamna Yusuf na ba da fifiko ga shirye-shiryen da suka shafi rayuwar al’ummar jihar kai tsaye, musamman wadanda ke fuskantar kalubalen kiwon lafiya.
Dantiye ya bayyana cewa ya ji dadin ganin farin ciki a fuskokin majinyatan da suka ci gajiyar tallafin tare da jaddada kudirin gwamnati na tallafawa marasa galihu musamman a lokacin rashin lafiya.
“Mun sadaukar da kai don taimakawa a duk inda aka fi bukata”
A jawabinsa, Babban jami’in kula da cututtuka masu yaduwa, Dokta Johnson Ochibo, ya ce rabon kayan agajin ga majinyatan asibitoci ya nuna jajircewar Gwamna Abba Kabir Yusuf wajen kyautata rayuwar al’ummar Kano, ya kara da cewa irin wadannan tsare-tsare na nuna yadda gwamnati ke kula da bukatun al’umma.
A yayin rabon kayayyakin tallafin, kwamishinan ya samu rakiyar babban sakataren ma’aikatar ayyuka na musamman, Sunusi Abbas.
Khadija Aliyu
-
Labarai3 days ago
Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai
-
Kasuwanci4 days ago
CBN Ya Sake Karya Farashin Dala Zuwa N1,101
-
Fasaha3 days ago
Shugaba Tinubu Ya Kaddamar Shirin Bada Bashin Kayyaki Ga ‘Yan Kasa
-
Labarai5 days ago
An Kwashe Mutane Da Dama Bayan Mummunar Ambaliyar A China
-
Fasaha5 days ago
Mutane 3 Sun Mutu a Salga a Kano
-
Labarai13 hours ago
Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano
-
Labarai5 days ago
Shugaban Hukumar Leken Asirin Isra’ila Ya Yi Murabus
-
Kasuwanci4 days ago
Gwamnatin Jihar Kwara Ta Dakatar Da Yanka Nama A Mahauta Na Kwanaki 3