Fasaha
Sanƙarau Ta Kashe Mutum 6 A Gombe
Akalla mutum shida ne suka rasu sakamakon kamuwa da cutar sanƙarau a Kananan Hukumomin Nafada da Funakaye a Jihar Gombe.
Kwamishinan Lafiya na jihar, Dokta Habu Dahiru ne, ya sanar da haka da yammacin ranar Alhamis.
Ya ce hukumar lafiya ta jihar ta gudanar da bincike tare da tabbatar da bullar cutar a kananan hukumomin biyu.
Ya ce an tabbatar da mutuwar mutum shida; mutum biyar a Karamar Hukumar Nafada, yayin da wani mutum daya ya rasu a Karamar Hukumar Funakaye.
A cewarsa sun samu rahoton bullar cutar ne a ranar 18 ga watan Fabrairu 2024, bayan yi es mutum 95 gwajin cutar a Babban Asibitin Garin Funakaye.
A cewar Kwamishinan, an sallami mutum 84 daga cikin mutum 95 da suka kamu da cutar, yayin da mutum shida ke ci gaba da karbar magani a asibiti.
Ya kara da cewar daga cikin wasu mutum 29 da aka yi gwaji, an samu mutum biyu dauke da cutar.
Gwamnan jihar, Muhammad Inuwa Yahaya, ya bayar da umarnin bayar da magunguna da tallafi ga asibitin don domin dakile yaduwar cutar.
Gwamnan ya umarci farfado da Cibiyar Dakile Cututtuka Masu Yaduwa (NCDC) a jihar.
Ya yi kira ga jama’ar jihar da kaucewa kwanciya cikin zafi da kuma cunkoso domin hakan na iya haifar da cutar sanƙarau.
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Labarai6 days ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa
-
Ilimi4 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura
-
Labarai4 days ago
An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya
-
Labarai6 days ago
An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas
-
Fasaha19 hours ago
Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno
-
Kasuwanci16 hours ago
CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati
-
Fasaha19 hours ago
Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet