Connect with us

Fasaha

Sanƙarau Ta Kashe Mutum 6 A Gombe

Published

on

Akalla mutum shida ne suka rasu sakamakon kamuwa da cutar sanƙarau a Kananan Hukumomin Nafada da Funakaye a Jihar Gombe.

Kwamishinan Lafiya na jihar, Dokta Habu Dahiru ne, ya sanar da haka da yammacin ranar Alhamis.

 

Ya ce hukumar lafiya ta jihar ta gudanar da bincike tare da tabbatar da bullar cutar a kananan hukumomin biyu.

Ya ce an tabbatar da mutuwar mutum shida; mutum biyar a Karamar Hukumar Nafada, yayin da wani mutum daya ya rasu a Karamar Hukumar Funakaye.

A cewarsa sun samu rahoton bullar cutar ne a ranar 18 ga watan Fabrairu 2024, bayan yi es mutum 95 gwajin cutar a Babban Asibitin Garin Funakaye.

A cewar Kwamishinan, an sallami mutum 84 daga cikin mutum 95 da suka kamu da cutar, yayin da mutum shida ke ci gaba da karbar magani a asibiti.

Ya kara da cewar daga cikin wasu mutum 29 da aka yi gwaji, an samu mutum biyu dauke da cutar.

Gwamnan jihar, Muhammad Inuwa Yahaya, ya bayar da umarnin bayar da magunguna da tallafi ga asibitin don domin dakile yaduwar cutar.

Gwamnan ya umarci farfado da Cibiyar Dakile Cututtuka Masu Yaduwa (NCDC) a jihar.

Ya yi kira ga jama’ar jihar da kaucewa kwanciya cikin zafi da kuma cunkoso domin hakan na iya haifar da cutar sanƙarau.

Labarai

Kasuwanci16 hours ago

CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati

Babban Bankin Najeriya CBN ya bayar da wa’adin ranar 7 ga watan  Yulin 2024 ga masu POS su kammala rajista...

Fasaha19 hours ago

Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno

  Gwamnatin jihar Borno ta fara aikin horas da malamai 1,949 a matakin farko da aka gano cewa suna iya...

Fasaha19 hours ago

Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet

  Babban Bankin Najeriya (CBN) ya umurci bankunan kasar su fara cirar kaso 0.5 cikin 100 na duk kuɗin da...

Labarai19 hours ago

An kashe Falasɗinawa 34,800 tun fara yaƙi – Ma’aikatar lafiyar Hamas

Ma’aikatar lafiya ta Hamas a Gaza ta ce an kashe Falasdinawa 34,789 a yankin tun ranar 7 ga watan Oktoba,...

Ilimi4 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta ci gaba da tallafawa harkokin koyo da koyarwa a Jami’ar Fasaha ta Gwamnatin...

Labarai4 days ago

An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya

Shugaban kungiyar masu noman rogo ta Najeriya (NCGA), Mustapha Othman Bakano, ya kaddamar da wani tsari na samar da kasuwa...

Labarai6 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai6 days ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Labarai6 days ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai1 week ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Mafi Shahara