Ilimi
Sheikh Daurawa Ya Yi Murabus Daga Shugabancin Hisba
Shugaban Hukumar Hisba na Jihar Kano, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa, ya yi murabus da mukaminsa.
Daurawa ya sanar da saukarsa daga shugabancin hukumar ne bayan kalaman gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf, ya yi na sukar yadda hukumar ke gudanar da ayyukanta na yaki da badala a jihar.
Daurawa, ya sanar da murabus dinsa daga shugabancin hukumar, a wani bidiyo da ya wallafa a shafinsa na Facebook da safiyar ranar Juma’a.
Kalaman gwamna Abba Gida-Gida, sun yamutsa hazo a jihar, inda wasu ke ganin kalaman nasa a matsayin wata gaba ta goyon bayan masu aikata badala a jihar.
Idan ba a manta ba hukumar Hisba a jihar ta fito da sabon salon yaki da baɗala, inda ta dinga kai samame wurare shakatawa da otal-otal tana kama masu yawon ta-zubar.
Daga bisani Murja ta yi layar bata daga gidan yari, lamarin da ya tayar da kura da haifar da cece-kuce musamman a kafafen sada zumunta.
Sai dai gwamnatin jihar a wani martani da ta yi, ta hannun Kwamishinan Yada Labaran jihar, Baba Dantiye, ya musanta wannan zargi da ake yi wa gwamnatin.
-
Labarai3 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi5 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha5 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai4 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai4 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai2 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai4 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar
-
Labarai4 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana