Connect with us

Ilimi

Tinubu Ya Umarci Dangote Da BUA Su Rage Farashin Siminti

Published

on

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya umarci kamfanin Dangote da BUA da su rage kudin farashin buhun siminti don samar wa al’umma sauki daga matsin rayuwa da ake fuskanta.

Ministan Ayyuka, Sanata David Umahi ne, ya bayyana hakan ga manema labarai jim kadan bayan ziyara da ya kai masana’antar siminti ta BUA da ke Sakkwato a ranar Alhamis.

 

Babban Darakta a kamfanin BUA, Alhaji Kabiru, ya ce a halin yanzu suna sayar da buhun siminti kan kudi Naira 6000, don cika alkawarin da suka yi daukar wa shugaban kasa cewa ba za su sayar da buhun siminti sama da 7000 ba.

“Game da batun farashin siminti, zan iya cewa har yanzu suna yin abin da ya dace kamar yadda suka tattauna da shugaban kasa

“Shugaban kasa ya jaddada batun dawo da farashin baya domin saukaka wa talaka.

“Ina so na kara musu kwarin gwiwa don su bi umarnin shugaban kasa domin mu cimma shirin samar da gidaje da kuma sabbin hanyoyin gina rayuwa kamar yadda shugaban kasa ya bukata,” in ji shi.

A baya-bayan nan dai kayayyaki sun yi tashin gwauron zabi a Najeriya, lamarin da ya sanya talakawa kokawa.

Farashin kudin buhun siminti ya ninka kudinsa na baya, inda a wasu jihohi ake sayar da shi daga Naira 10,000 zuwa 15,000.

A gefe guda kuwa, kungiyoyin kwadago na NLC da TUC sun gudanar da zanga-zangar kwanaki biyu a ranar Talata da Laraba, don neman gwamnatin tarayya yi wani abu kan tsadar rayuwa a Najeriya.

Shugaba Tinubu dai ya roki ‘yan Najeriya da su kara hakuri kan yanayin da ake ciki, wanda a cewarsa yana aiki tukuru don samar wa da talaka sauki daga halin da ake ciki.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai16 hours ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai18 hours ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai19 hours ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi19 hours ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai2 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai2 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai3 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai3 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai3 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara