Labarai
Cutar Lassa Ta Kashe Mutum 4 A Asibitin Soji A Kaduna
Jami’an lafiya uku da wani mara lafiya sun rasu sakamakon bullar cutar da ake zargin Zazzabin Lassa ce a Babban Asibitin Sojoji na 44 da ke Kaduna.
Wata majiya a asibitin ta ce daga cikin jami’an lafiyan da suka rasu har da wata mai yi wa kasa hidima (NYSC) da ake aiki a asibitin sojojin
Wata sanarwa da Mukaddashin Kwamandar Sashen Kiwon Lafiya na Rundunar Sojin Kasa ta Najeriya, Birgediya S.O Okoigo, ta ce, wasu karin mutane ma kwance cikin mawuyacin hali a sakamakon zazzabin Lassa da ake zargi.
“Wani mara lafiya da ma’aikata suka a Sashen Kula da Lafiya na Gaggawa a Asibitin Soji na 44 NARHK sun rasu, a yayin da wasu ke cikin mawuyacin hali,” inji sanawar da Birgediya S.O Okoigo, ya aike wa cibiyoyin lafiya na rundunar.
Ta ci gaba da cewa, jamia’an lafiyan sun rasu ne a garin jinyar mara lafiyan da ake zargi da cutar, “a tsawon kwanaki 10 da suka wuce, inda ya nuna alamar cutar kafin daga bisani rai ya yi halinsa.”
Ya ce, “An rufe sashen kula da lafiya na gaggawan domin kashe kwayoyinc utar, sannan an tsaurara matakan kariya domin hana yaɗuwarta.
“An tura samfurin kwayar cutar zuwa cibiyar gwajin kwayar cuta ta Hukumar Hana Yaduwar Cututtuka ta Kasa (NCDC) da ke Kano, domin gudanar da bincike.
“An gayyato jami’an tantance kwayar cuta na Gwamnatin Jihar Kaduna domin gudanar da bincike sannan an dauki matakan kariya domin takaita yaduwar cutar.
“Haka zalika za a samar da alluran riga-kafi domin dakile yaduwar wannan cuta.”
-
Fasaha6 days ago
Shugaba Tinubu Ya Kaddamar Da Kamfanin Sarrafa Sinadarin Batira a Lafiya
-
Ilimi3 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Labarai2 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai6 days ago
Mbappe ya sanar da cewa zai bar PSG a karshen kaka
-
Fasaha3 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai3 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai3 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai3 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana