Connect with us

Labarai

An Kashe Jagoran Harin NDA Da Sace Daliban Birnin Yauri

Published

on

Sojoji sun kashe kasurgumin dan bindiga, Boderi, wanda ya kitsa harin da aka kai makarantar horas da sojoji ta NDA da ke Kaduna.

Boderi ne kuma ya kitsa hari da kuma sace dalibai a Jami’ar Greenfield da ke jihar, da kuma ’yan matan makarantar sakandaren Birnin Yauri da ke Jihar Kebbi, kamar yadda kakakin rundunar, Manjo-Janar Onyema Nwachukwu, ya sanar.

Sanarwar ta ce cewa a ranar Laraba aka kashe Boderi ne tare da wani shugaban ’yan bindiga mai suna Bodejo a kan hanyar Bada–Riyawa da ke kan hanyar Kaduna zuwa Birnin Gwari.

“Majiyoyin leken asiri sun ba da rahoton cewa an kashe kasurgumin dan bindiga Boderi wanda ya kitsa sace daliban Birnin Yauri, Jami’ar Greenfield da kuma NDA, tare da wani mai suna Bodejo.

“Ana ci gaba da kokarin tabbatar da hakan ta hanyar amfani da wasu hanyoyi,” in ji sanarwar.

A cewarsa, kun kwato babura 19 da ’yan ta’addan suka gudu suka bari da wasu abubuwa, kuma an kona su.

a wani samame na daban da sojoji suka kai a yankin, “’yan ta’addan da suka yi amfani da shanu a matsayin garkuwa, sun bude musu wuta, amma suka mayar da martani cikin gaggawa.

“A yayin musayar wutar ta kusan awa daya, sojoji sun kashe biyu daga cikin ’yan ta’addan tare da kwato bindiga kirar AK 47 guda 1, da sauran abubuwa.

“Sai dai kuma an kashe wasu daga cikin dabbobin satan da da ’yan ta’addan ke amfani da su a matsayin garkuwa.

“Sojoji na ci gaba da bin diddigin ’yan ta’addan da suka tsere da kuma aikinsu na samar da tsaro a yankin.”
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai6 hours ago

Ma’aikatan Ceto Na Cigaba Da Neman Jirgin Shugaban Kasar Iran Da Ya Bace

Da yammacin yau lahadi ne tarin ma’aikatan ceto suka bazama wajen aiki gano jirgi mai saukar ungulu dauke da shugaba...

Labarai4 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai4 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai4 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi4 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai4 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai5 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai6 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai6 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai6 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Mafi Shahara