Connect with us

Labarai

An katse wa majalisar dokokin Ghana lantarki saboda bashin kuɗin wuta

Published

on

Kamfanin wutar lantarki na Ghana (ECG) ya katse wutar lantarkin majalisar dokokin ƙasar a ranar Alhamis saboda gaza biyan bashin kuɗi cedi miliyan 23 da ake bin majalisar.

Wanda yawan kuɗin ya kai dalar Amurka miliyan 1.8.

Katsewar ya kawo cikas ga muhawarar da ake tafkawa a majalisar kan jawabin da shugaban kasar ya yi, inda ƴan majalisar suka rika rera taken “Dumsor, dumsor,” wato matsalar wutar lantarki.

Kafofin yada labarai na cikin gida sun ruwaito cewa duk da cewa an kunna janaretan majalisar domin samar da lantarki a lokacin, sauran sassan ginin majalisar sun kasance babu wutar a yawancin ranar.

Daraktan sadarwa na kamfanin wutar lantarki, William Boateng ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa ya dauki matakin katse wutar ne saboda ƙin amincewa da majalisar dokokin kasar ta yi na “girmama sanarwar bukatar biyan bashin”.

An dai mayar da wutar lantarkin ne bayan da majalisar ta biya cedi miliyan 13 tare da yin alkawarin sasanta sauran basukan nan da mako guda.

Daraktan sadarwa na ECG ya bayyana cewa haka za su katse wutar lantarki duk wanda ake bi bashi da kuma ƙin biyan bashin.

Kamfanin wutar lantarki na Ghana na fuskantar matsalar kudi, lamarin da ke janyo katsewar wutar lantarkin akai-akai daga abokan huldar da yake bi bashi a yayin da ake fama da ƙarancin wutar saboda kalubalen tattalin arziki.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Kasuwanci18 hours ago

CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati

Babban Bankin Najeriya CBN ya bayar da wa’adin ranar 7 ga watan  Yulin 2024 ga masu POS su kammala rajista...

Fasaha20 hours ago

Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno

  Gwamnatin jihar Borno ta fara aikin horas da malamai 1,949 a matakin farko da aka gano cewa suna iya...

Fasaha21 hours ago

Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet

  Babban Bankin Najeriya (CBN) ya umurci bankunan kasar su fara cirar kaso 0.5 cikin 100 na duk kuɗin da...

Labarai21 hours ago

An kashe Falasɗinawa 34,800 tun fara yaƙi – Ma’aikatar lafiyar Hamas

Ma’aikatar lafiya ta Hamas a Gaza ta ce an kashe Falasdinawa 34,789 a yankin tun ranar 7 ga watan Oktoba,...

Ilimi4 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta ci gaba da tallafawa harkokin koyo da koyarwa a Jami’ar Fasaha ta Gwamnatin...

Labarai4 days ago

An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya

Shugaban kungiyar masu noman rogo ta Najeriya (NCGA), Mustapha Othman Bakano, ya kaddamar da wani tsari na samar da kasuwa...

Labarai6 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai6 days ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Labarai6 days ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai1 week ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Mafi Shahara