Connect with us

Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Bada Buhunan Abinci 36,000 Ga Jihar Borno

Published

on

Gwamnatin tarayya ta baiwa gwamnatin jihar Borno tallafin buhunan abinci dubu talatin da shida da dari biyu da goma sha hudu masu nauyin kilogiram hamsin.

Da take gabatar da kayayyakin ga Gwamnan Jihar Farfesa Babagana Zulum, Darakta Janar ta Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta kasa NEMA, Hajiya Zubaida Umar ta ce kayayyakin na daga cikin  tan dubu arba’in da biyu  na hatsi da aka fitar daga runbun gwamnati.

Shugabar hukumar wacce darakta janar na shiyyar Arewa maso Gabas, Malam Yakubu Sulieman, ya wakilce ta, ta bayyana cewa bada tallafin kayan abinci na daga cikin shirin rage tasirin tabarbarewar tattalin arzikin da ake fama da shi a yankin.

Shugaban kasa ya amince da fitar da kayayyakin abinci har ton 42,000 daga runbun gwamnatin tarayya da ke karkashin kulawar ma’aikatar noma da samar da abinci ta, a don haka mun zo ne domin mika kayayyakin ga gwamnatin jihar Borno inda za ta  raba ga wadanda suka cancanta”.

A jawabinsa, Gwamnan Jihar Borno, Babagana Zulum, ya jinjinawa  gwamnatin tarayya bisa wannan karamci ga al’ummar jihar, musamman wadanda rikicin Boko Haram ya shafa.

Ya kuma baiwa shugaban kasa da hukumar bada agajin gaggawa ta kasa tabbacin cewa za a raba kayan abincin da aka bayar ga marasa galihu a jihar.

Ina kuma tabbatar muku da cewa ba za a samu karkatar da kayayyakin a jihar Borno ba, za a raba bisa cancanta ga al’ummar jihar.” Inji Zulum.

Gwamna Zulum ya kuma yabawa gwamnatin tarayya bisa bada gudunmawa a yunkurin da gwamnatin sa ke yi na sake tsugunar da wadanda rikici ya daidaita.

Shi ma a nasa jawabin,  Darakta Janar na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar SEMA, Dokta Muhammed Barkindo ya ce za a ba da fifiko ga gidaje suka rasa mahaifinsu da marasa lafiya da kuma masu fama da lalurar nakasa.

Kayayyakin da aka bayar sun hada da buhunan Masara 11,880, buhunan dawa 19,440 da buhunan Gero 5,130.

 

Dauda Iliya 

Labarai

Labarai2 days ago

Matasan Kauru Sun Yi Allah-wadai da Mulkin Ƙarfi, Sun Buƙaci Adalci da Haɗin Kai

  Daga Yusuf Zubairu Wata ƙungiyar matasa a Ƙaramar Hukumar Kauru ta Jihar Kaduna ta bayyana cewa shugabanci na bai-ɗaya...

Labarai3 days ago

Ma’aikatar Lafiya Ta Fara Daukar Jami’an Kula da Lafiya na Ƙasa a Jigawa

Usman Muhammad Zaria  Ma’aikatar Lafiya ta kasa karkashin shirin kula da lafiya na SWAP ta fara aikin daukar Jami’an Kula...

Labarai1 week ago

Baragurbi a Aikin Jarida na Barazana ga Sahihancin Kafafen Yada Labarai – Shugaban NUJ-FRCN

Shugaban Ƙungiyar ’Yan Jarida ta Najeriya (NUJ), reshen FRCN Kaduna, Kwamared Umar Adamu Sarkinfada, ya bayyana cewa mummunan aikin jarida...

Labarai2 weeks ago

Ƙaruwa a Shan Abubuwan Sha Masu Ƙara Ƙarfi na Haddasa Damuwar Lafiya a Kano

Abubuwan sha masu ƙara ƙarfi, waɗanda aka fi sani da energy drinks ko energizers, na ƙara samun karɓuwa a faɗin...

Labarai2 weeks ago

Shugaba Tinubu Ya Taya CPSO Usman Shugaba Murnar Cika Shekara 45 da Haihuwa

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya Kwamishinan ‘Yan Sanda, Usman Musa Shugaba, wanda shi ne Babban Jami’in Tsaron ‘Yan...

Labarai2 weeks ago

TSARO: Gwamnan Jihar Neja Ya Nuna Alhini Kan Harin ‘Yan Ta’adda a Al’ummomin Borgu

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya bayyana matuƙar baƙin cikinsa kan harin ‘yan ta’adda da aka kai wa wasu...

Labarai2 weeks ago

Allah Ya Jikan Jarman Kauru Da Ke Jihar Kaduna

Mun sami labarin rasuwar tsohon Kwamishinan Ilimi na Jihar Kaduna, Malam Suleiman Lawal Jarman Kauru. Malam Suleiman Lawal, mai shekaru...

Labarai2 weeks ago

Gwamnatin Kano Ta Faɗaɗa Damar Tattalin Arziki ga Mata da Masu Buƙata Ta Musamman

An kammala kasuwar baje kolin mata ta tsawon kwanaki huɗu, wadda Ma’aikatar Harkokin Mata, Yara da Masu Buƙata Ta Musamman...

Labarai2 weeks ago

Rundunar Tsaro Ta Haɗin Gwiwa Ta Hallaka ’Yan Bindiga 150

Rundunar tsaro ta haɗin gwiwa da ta ƙunshi Sojojin Nijeriya, Hukumar Tsaron Farin Ciki (DSS), ’Yan Sanda da sauran hukumomin...

Ilimi2 weeks ago

Gwamnatin Neja Ta Amince da Sake Buɗe Makarantun Gwamnati da Masu Zaman Kansu daga 12 ga Janairu

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya amince da sake buɗe dukkan makarantun gwamnati da masu zaman kansu a faɗin...

Mafi Shahara