Connect with us

Kasuwanci

Gwamnati Ta Kaddamar Da Rabon Hatsi Tan 42,000 A Sakkwato

Published

on

Gwamnatin Tarayya, ta ƙaddamar da rabon tan 42,000 na hatsi ga mabuƙata a Jihar Sakkwato.

Rabon wani ɓangare ne na umarnin shugaba Bola Tinubu, na tallafa wa marasa ƙarfi da abinci a halin matsin rayuwa da ake fuskanta a Najeriya.

Ministan Yaɗa Labarai, Mohammed Idris ne, ya bayyana hakan ranar Lahadi a shafinsa na X (Twitter).

Ya ce “Na bi sahun gwamnan Sakkwato, Ahmed Aliyu da abokan aikina, ministan noma da samar da abinci da ƙaramin minista Sabi Aliyu wajen ƙaddamar da rabon.”

Hukumar Bayar da Agaji ta Kasa (NEMA), za ta sanya ido kan rabon tare da taimakon hukumomin tsaro domin tabbatar da gaskiya da adalci.

A cewar ministan, kowace jiha a faɗin Najeriya za ta ci gajiyar rabon “Za mu tabbatar mun bayar da ƙarin bayani kan shirin.”

Tun farkon watan Maris ne, Shugaba Bola Tinubu, ya bayar da umarnin fara raba hatsin a faɗin jihohin Najeriya 36 da ke ƙasar nan.

Wannan dai na zuwa ne bayan cire tallafin man fetur da Shugaba Tinubu ya yi wata 10, bayan karɓar mulki a watan Mayun 2023.

Cire tallafin ya janyo hauhawar farashin kayayyakin masarufi, lamarin da ya kai ga gudanar da zanga-zanga a wasu jihohin ƙasar nan.

NASIR MALAMI/Wababe

Labarai

Labarai12 hours ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai3 days ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Fasaha3 days ago

An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar

Kungiyar Malaman Jami’ar Jihar Sakkwato ASUU-SSU ta yi kira ga gwamnatin Jihar ta duba halin da kungiyar ke ciki da...

Kasuwanci3 days ago

Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

  Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin...

Ilimi3 days ago

Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark,...

Labarai6 days ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu. Jakadan...

Labarai1 week ago

Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar...

Ilimi1 week ago

Daliban Jihar Kebbi Da Ke Kasashen Waje Za Su Sami Tallafin Naira Miliyan 309

Gwamnatin jihar Kebbi, ta amince da kashe sama da Naira miliyan Dari Uku da Tara, domin biyan tallafin karatu na...

Kasuwanci1 week ago

Kwari Masu Lalata Amfanin Gona Sun Mamaye Gonakin Tumatur A Kano

Shugaban kungiyar manoma ta jihar Kano, AFAN, Abdullahi Maibreadi, ya bukaci gwamnati a dukkan matakai da su taimaka wa manoma...

Mafi Shahara