Connect with us

Labarai

Za A Samarda Tsaro Lokacin Bukin Sallah A Nasarawa – Kwamishina

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Nasarawa ta ce an samar da isassun matakan tsaro domin tabbatar da gudanar da bukukuwan Sallah ba tare da tangarda ba a jihar.

 

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Umar Shehu Nadada ya bayyana haka a wata sanarwa da ya sanyawa hannu kuma aka rabawa manema labarai a garin Lafia babban birnin jihar.

 

Sanarwar ta bayyana cewa Kwamishinan ‘yan sandan a lokacin da yake taya al’ummar Musulmi murnar kammala azumin watan Ramadan na bana tare da yi wa dukkan musulmi fatan bukukuwan Sallah lafiya. Ya kuma yi kira ga al’ummar jihar da su yi amfani da lokacin bukukuwan domin yin addu’o’in zaman lafiya da ci gaban jihar da kasa baki daya.

 

Kwamishinan ‘yan sandan ya yi kira ga malaman addini, masallata da mazauna jihar da su ba ‘yan sanda da sauran hukumomin tsaro hadin kai, domin ya tabbatar da cewa an yi kokarin inganta tsaro a lokacin bikin sallah karama.

 

Sanarwar ta kuma umurci dukkan kwamandojin ‘yansanda na yankin da shugabannin sassan da kuma jami’an ‘yan sanda na sassan jihar da su rika sanya ido domin kare rayuka da dukiyoyin jama’a, da samar da tsaro a duk wuraren ibada da na shakatawa da kuma kai samame a wuraren da aka gano akwai matsala.

 

Don haka kwamishinan ‘yan sandan ya umarci al’ummar jihar da su kasance masu zaman lafiya da gudanar da bukukuwa cikin kwanciyar hankali.

 

Idan kuma wata matsala ta taso, ana kira ga jama’a kada suyi kasa a gwiwa wajen kiran wadannan lambobin waya kamar haka: 08036157659, 08032564469, 08112692680 da 08104441179.

Rel/Aliyu Muraki/Lafia/Wababe

Labarai

Labarai4 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai4 hours ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Labarai17 hours ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai3 days ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Fasaha3 days ago

An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar

Kungiyar Malaman Jami’ar Jihar Sakkwato ASUU-SSU ta yi kira ga gwamnatin Jihar ta duba halin da kungiyar ke ciki da...

Kasuwanci3 days ago

Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

  Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin...

Ilimi3 days ago

Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark,...

Labarai6 days ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu. Jakadan...

Labarai1 week ago

Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar...

Mafi Shahara