Connect with us

Kasuwanci

‘Yan Sanda Zasu Tabbatar Da Tsaro A Lokacin Bukukuwan Sallah A Kano

Published

on

 

 

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ba da tabbacin a shirye ta ke na tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin ‘yan kasa kafin, lokacin da bayan bukukuwan Sallah karama da za a fara gobe laraba.

 

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Mohammad Hussein Gumel ne ya bayyana hakan a lokacin wani taron masu ruwa da tsaki da sarakunan gargajiya, malamai da sauran masu ruwa da tsaki da suka shafi tabbatar da tsaro.

 

Ya ce dukkan hukumomin tsaro za su kasance cikin shiri a kowane lungu da sako da niyyar tabbatar da gudanar da bukukuwan Sallah lamui lafiya.

 

CP Mohammad Hussein Gumel ya lura cewa rundunar ta riga ta tattara dukkan rahotannin sirrin tsaro da ake bukata, don haka akwai bukatar a aiwatar da tsarin da zai tabbatar da zaman lafiya.

 

Ya yi kira ga sarakunan gargajiya da malamai da su hada kai da jami’an tsaro, yana mai jaddada cewa jihar Kano ta samu zaman lafiya sakamakon hadin kai da ke tsakanin jama’a da jami’an tsaro.

 

“Mun tsara dabarun inganta tsaro, kuma muna da kwarin gwiwar cewa shawarwarin za su yi aiki yadda ya kamata wajen ganin mun shaida bukukuwan Sallah lafiya kalau.”

 

A jawabansu daban daban wakilan sarakunan Bichi da Gaya Alhaji Nura Ahmed madakin Bichi da Alhaji Bashir Albasu, makaman Gaya sun yaba da kokarin da kuma jajircewar rundunar ‘yan sandan Kano na ci gaba da aiki babu kama hannun yaro wajen dakile ayyukan miyagun ayyuka a jihar.

 

“Wannan taron ya dace da lokacin da ya dace, saboda batun tsaro alhakin kowa ne, don haka akwai bukatar mu hada kai don tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi a cewar wakilan sarakunan da suka halarci taron.

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO/Wababe

Labarai

Labarai5 hours ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai2 days ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Fasaha3 days ago

An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar

Kungiyar Malaman Jami’ar Jihar Sakkwato ASUU-SSU ta yi kira ga gwamnatin Jihar ta duba halin da kungiyar ke ciki da...

Kasuwanci3 days ago

Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

  Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin...

Ilimi3 days ago

Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark,...

Labarai5 days ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu. Jakadan...

Labarai1 week ago

Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar...

Ilimi1 week ago

Daliban Jihar Kebbi Da Ke Kasashen Waje Za Su Sami Tallafin Naira Miliyan 309

Gwamnatin jihar Kebbi, ta amince da kashe sama da Naira miliyan Dari Uku da Tara, domin biyan tallafin karatu na...

Kasuwanci1 week ago

Kwari Masu Lalata Amfanin Gona Sun Mamaye Gonakin Tumatur A Kano

Shugaban kungiyar manoma ta jihar Kano, AFAN, Abdullahi Maibreadi, ya bukaci gwamnati a dukkan matakai da su taimaka wa manoma...

Mafi Shahara