Labarai
Guguwa ta kashe mutum daya, ta kuma lalata gidaje sama da 100 a Nasarawa
Wata kakkarfar Guguwar ta kashe mutum daya tare da jikkata wasu da dama tare da lalata gidaje sama da dari a Agbashi da ke karamar hukumar Doma a jihar Nasarawa.
Da yake tabbatar da faruwar lamarin ga manema labarai, mataimakin shugaban karamar hukumar Doma Mista John Bako – Ari, ya ce abin takaicin ya faru ne a ranar Talata da yamma.
A cewarsa, sama da gidaje dari ne aka lalata da suka hada da babban masallacin Agbashi, wani bangare na makarantar furamare ta Agbashi da sauran kayayyakin more rayuwa da dama na jama’a.
“A gaskiya guguwar ta lalata gidaje sama da 100 da suka hada da, masallaci da kuma makarantar Firamare, lamarin ya faru ne jiya da yamma,” inji shi.
Shima da yake magana akan lamarin, mukaddashin shugaban kungiyar ci gaban Agbashi, Mista Anthony Oshinyeka, mukaddashin shugaban kungiyar ci gaban yankin, ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici.
Ya kuma yi kira ga gwamnati da ta gaggauta kawo dauki domin dakile mummunar barnar da al’ummar Agbashi ke fama da shi.
Mukaddashin Shugaban kungiyar ya nemi da a gaggauta bada kayan agaji daga gwamnati da masu hannu da shuni ga al’ummomin da abin ya shafa.
Aliyu Muraki/Lafia/Wababe
-
Labarai3 days ago
Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa
-
Labarai6 days ago
Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano
-
Fasaha3 days ago
An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar
-
Labarai18 hours ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa
-
Kasuwanci3 days ago
Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno
-
Labarai4 hours ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Ilimi3 days ago
Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert