Ilimi
Daliban Makarantar Kuriga Sun Shaki Iskar ‘Yanci – Uba Sani
Gwamnatin jihar Kaduna ta sanar da sakin yara ‘yan makaranta dari biyu da tamanin da bakwai 287 da aka yi garkuwa da su daga Kuriga da ke karamar hukumar Chikun ta jihar
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun gwamnan jihar Uba Sani.
Sanarwar ta ce “Ina so in sanar da cewa an sako yaranmu na makarantar Kuriga, muna godiya ta musamman ga mai girma shugaban mu, Bola Ahmed Tinubu, bisa ba da fifiko ga tsaro da tsaron ‘yan Nijeriya, musamman kokarin da ya yi na ganin an sako ‘ya’yan makarantar Kuriga da aka sace ba tare da wani lamuni ba”.
Gwamnan ya kuma yaba da jajircewar hafsoshin sojojin Najeriya na ganin an samu nasarar sako yaran.
“Muna kuma gode wa daukacin ‘yan Najeriya bisa addu’in da suka yi na ganin Allah Ya dawo da yaran cikin koshin lafiya, lallai wannan ranar farin ciki ce. Muna godiya ga Allah Madaukakin Sarki.”
Idan dai za a iya tunawa, a ranar 7 ga watan Maris, 2024, ‘yan bindiga suka sace ‘yan makarantar firamare da na Sakandaren Gwamnati da ke Kuriga, inda suka kai su dajin.
Masu garkuwa da mutanen sun bukaci a bada kudin fansa na Nera milyan dubu daya, yayin da suka ba da wa’adin ranar 27 ga Maris, 2024, don biyan kudin.
Aminu Dalhatu
-
Labarai3 days ago
Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai
-
Kasuwanci4 days ago
CBN Ya Sake Karya Farashin Dala Zuwa N1,101
-
Fasaha3 days ago
Shugaba Tinubu Ya Kaddamar Shirin Bada Bashin Kayyaki Ga ‘Yan Kasa
-
Labarai5 days ago
An Kwashe Mutane Da Dama Bayan Mummunar Ambaliyar A China
-
Fasaha5 days ago
Mutane 3 Sun Mutu a Salga a Kano
-
Labarai16 hours ago
Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano
-
Labarai5 days ago
Shugaban Hukumar Leken Asirin Isra’ila Ya Yi Murabus
-
Kasuwanci4 days ago
Gwamnatin Jihar Kwara Ta Dakatar Da Yanka Nama A Mahauta Na Kwanaki 3