Connect with us

Ilimi

An Bukaci Masu Hannu Da Shuni Su Rika Taimakawa Marasa Galihu a Watan Ramadan

Published

on

An bukaci masu hannu da shuni da su taimaka wa marasa karfi dake cikin al’umma domin su gudanar da azumin watan Ramadan cikin sauki.

Marafan Yamman Zazzau, Alhaji Adamu Ubaidullah ya yi kiran lokacin da ya zanta da wakilin Radio Najeriya a zaria.

Ya bayyana cewa idan aka yi la’akari da matsin tattalin arzikin kasa ke fuskanta ya zama wajibi al’umma su rungumi dabi’an taimaka wa junan su, musamman a wannan wata na azumin watan Ramadan.

Marafan Yamman na Zazzau ya ce akwai dimbin laba ga duk mutumin da ya ciyar da wani a wannan lokaci, musamman ganin yadda kayan masarufi ya yi tsada ta yadda mutane da dama basa iya ciyar da iyalan su.

Alhaji Adamu Ubaidullahi ya kuma shawarci jama’a da su yi amfani da wannan watan mai albarka wajen yin addu’o’in Allah ya kawo wa kasar nan mafita,musamman ta fuskar rashin tsaro da kuma magance talauci.

Ya kuma bukaci gwamnatoci a dukkan matakai da su maida hankali wajen taimakawa kananan manoma domin su iya gudanar da mona idan damina ta fadi.

Ubaidullahi ya bayyana cewa dole sai gwamnati ta tallafawa manoma kasancewar kayan aikin noma ya yi matukar tsada ga kuma rashin ratso dake neman hana yin noman.

Ya kara da cewa kamata ya yi gwamnati ta sa hannun sarakunan gargajiya yayin taimaka wa manoman kasancewar sune suka san manoman gaskiya ba manoman biro ba.

Marafan Yamman Zazzau ya yaba wa maimartaba sarkin zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli bisa jajircewar da ya yi na samar da sauye-sauye domin ciyar da masarautar Zazzau gaba.

A don haka sai ya bukaci al’ummar masarautar Zazzau da su gaba da baiwa maimarta sarkin na Zazzau goyon baya da hadin kai domin ya sami karin karfin gwiwar samar da alhairai ga masarautar.

INT/HALIRU HAMZA

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai18 hours ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Ilimi20 hours ago

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu. Jakadan...

Labarai3 days ago

Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar...

Ilimi3 days ago

Daliban Jihar Kebbi Da Ke Kasashen Waje Za Su Sami Tallafin Naira Miliyan 309

Gwamnatin jihar Kebbi, ta amince da kashe sama da Naira miliyan Dari Uku da Tara, domin biyan tallafin karatu na...

Kasuwanci3 days ago

Kwari Masu Lalata Amfanin Gona Sun Mamaye Gonakin Tumatur A Kano

Shugaban kungiyar manoma ta jihar Kano, AFAN, Abdullahi Maibreadi, ya bukaci gwamnati a dukkan matakai da su taimaka wa manoma...

Fasaha3 days ago

Shugaba Tinubu Ya Kaddamar Shirin Bada Bashin Kayyaki Ga ‘Yan Kasa

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya ƙaddamar da kashin farko na tsarin karɓar bashin kaya ga ƴan ƙasar. Bayanin hakan na...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Jihar Kaduna Ta Rufe Bankin UBA Kan Kin Biyan Haraji

Hukumar Tara Kudaden Haraji ta Jihar Kaduna (KADIRS) ta raufe rassan bankin UBA kan kin biyan harajin Naira miliyan 14....

Labarai4 days ago

Mutum Biyar Sun Mutu Cikin Kwale-Kwalen ƴan Ci-Rani

Mutum biyar har da yaro sun mutu yayin da suke ƙoƙarin tsallake hanyar ruwa da ta ratsa Ingila da safiyar...

Kasuwanci4 days ago

CBN Ya Sake Karya Farashin Dala Zuwa N1,101

Babban Bankin Nigeria CBN ya sake sanar da matakin karya farashin dala daga N1,251 zuwa N1,101. CBN ya bayyana haka...

Ilimi4 days ago

Ƴan Sanda Za Su Yi Bincike Kan Makarantar Leads British

Rundunar ƴan sanda a babban birnin tarayya Abuja ta ce ta aika tawagar jami’anta zuwa makarantar Leads British bayan bidiyon...

Mafi Shahara