Labarai
Mataimakin Shugaban Tanzaniya Na Barazanar Yin Murabus Saboda Matsalar Karancin Ruwa
Mataimakin shugaban ƙasar Tanzaniya, Phillip Mpango ya yi barazanar sauka daga muƙaminsa saboda matsalar ƙarancin ruwan sha da aka daɗe ana fama da ita a lardin Mwanga da ke arewacin ƙasar.
Mista Mpango ya zargi ƴan kwangilar da ke kula da muhimmin aikin samar da ruwan sha a yankin na ɗaukan lokaci kafin kammala shi.
Shirin na sama da dala dubu 100 an soma shi ne kusan shekara 20 da ta gabata, a cewar Mista Mpango.
“Idan har aikin nan ba zai samar da ruwa ba ga mutanen yankin nan da watan Yuni, zan sauka.” Inji Mista Mpango.
“Ba zan sake zuwa nan na faɗa wa jama’a su ƙara hakuri ba, ruwa shi ne rayuwa,” ya ce.
A cewar jami’an gwamnati da suka yi wa Mista Mpango rakiya zuwa Mwanga a ranar Alhamis, an yi kashi 90 cikin 100 na aikin samar da ruwan.
-
Labarai24 hours ago
NAHCON Ta Jinjinawa Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Bisa Shirye-shiryen Hajjin Bana
-
Ilimi5 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura
-
Labarai23 hours ago
Amurka Ta Dakatar Da Kudurin Kai Jirgin Bama-Bamai Zuwa Isra’ila
-
Labarai6 days ago
An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya
-
Fasaha2 days ago
Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno
-
Kasuwanci2 days ago
CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati
-
Fasaha2 days ago
Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet
-
Labarai2 days ago
An kashe Falasɗinawa 34,800 tun fara yaƙi – Ma’aikatar lafiyar Hamas