Connect with us

Labarai

Zaben Senegal : Jami’yyar Adawa Ce Ke Kan Gaba

Published

on

Sakamakon farko na zaben shugaban kasar Senegal na nuna dan takarar jam’iyyar adawa Bassirou Diomaye Faye ne ke kan gaba, lamarinn da ya sanya magoya bayansa fita kan tituna don fara nuna murnar nasara a zaben, ko da yake babban abokin hamayyarsa na jam’iyyar da ke mulki ya ce sai an gudanar da zaben zagaye na biyu ne za a iya tantance wanda yayi nasara.

Tuni dai akalla ‘yan takara 5 daga ciki 19 da ke fafatawa a zaben, suka fidda sanarwar taya Faye murna, duk da ya ke tsohon firai ministan kasar Amadou Ba da ke takara a jam’iyar da ke mulki ya ce ya yi wuri mutane su fara murnar sakamakon farko na zaben.

 

Miliyoyin mutane ne dai suka kada kuri’ar zaben shugaban Senegal na biyar a tarihi, don zabo wanda zai maye gurbin Shugaba Macky Sall da gwamnatinsa ta sha suka kan rashin samar da tsarin saukaka matsin tattalin arziki.

A cewar kafar talabijin din kasar, kashi 71 na yawan masu kada kuri’a miliyan 7 da dubu dari 3 ne suka yi zabe a kasar da ke da akalla yawan mutane miliyan 18.

 

Sakamakon farko na zaben da aka bayyana a gidan talabijin din kasar ya nuna cewa Faye ne ke kan gaba, lamarin da ya sa magoya bayansa fara gudanar da bukukuwa a titunan Dakar babban birnin kasar.

Kawo yanzu dai ba a tan-tance yawan adadin sakamakon rumfunan zabe nawa ne aka kirga ba, daga cikin dubu 15 da dari 633.

 

A gobe Talata ce ake sa ran fidda sakamakon zaben da dan takara ke bukatar lashe kashi 50 na yawan kuri’un da aka kada kafin yin nasara, ko kuma a je zagaye na biyu.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai16 hours ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Ilimi18 hours ago

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu. Jakadan...

Labarai3 days ago

Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar...

Ilimi3 days ago

Daliban Jihar Kebbi Da Ke Kasashen Waje Za Su Sami Tallafin Naira Miliyan 309

Gwamnatin jihar Kebbi, ta amince da kashe sama da Naira miliyan Dari Uku da Tara, domin biyan tallafin karatu na...

Kasuwanci3 days ago

Kwari Masu Lalata Amfanin Gona Sun Mamaye Gonakin Tumatur A Kano

Shugaban kungiyar manoma ta jihar Kano, AFAN, Abdullahi Maibreadi, ya bukaci gwamnati a dukkan matakai da su taimaka wa manoma...

Fasaha3 days ago

Shugaba Tinubu Ya Kaddamar Shirin Bada Bashin Kayyaki Ga ‘Yan Kasa

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya ƙaddamar da kashin farko na tsarin karɓar bashin kaya ga ƴan ƙasar. Bayanin hakan na...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Jihar Kaduna Ta Rufe Bankin UBA Kan Kin Biyan Haraji

Hukumar Tara Kudaden Haraji ta Jihar Kaduna (KADIRS) ta raufe rassan bankin UBA kan kin biyan harajin Naira miliyan 14....

Labarai4 days ago

Mutum Biyar Sun Mutu Cikin Kwale-Kwalen ƴan Ci-Rani

Mutum biyar har da yaro sun mutu yayin da suke ƙoƙarin tsallake hanyar ruwa da ta ratsa Ingila da safiyar...

Kasuwanci4 days ago

CBN Ya Sake Karya Farashin Dala Zuwa N1,101

Babban Bankin Nigeria CBN ya sake sanar da matakin karya farashin dala daga N1,251 zuwa N1,101. CBN ya bayyana haka...

Ilimi4 days ago

Ƴan Sanda Za Su Yi Bincike Kan Makarantar Leads British

Rundunar ƴan sanda a babban birnin tarayya Abuja ta ce ta aika tawagar jami’anta zuwa makarantar Leads British bayan bidiyon...

Mafi Shahara