Connect with us

Fasaha

‘Yan Sanda Sun Kama Direban Da Ya Dauki Bajimi A Kujerar Fasinja

Published

on

Jami’an ’yan sanda sun kama wani direba mai suna Lee Meyer saboda daukar bajimi a kujerar fasinja ta gaba wadda aka kebe don dan Adam.

Bajimin nau’in Watusi mai girman kaho ’yan sandan birnin Norfolk a Gundumar Nebraska da ke Amurka ne suka kama direban bayan samun korafin da aka yi musu game da bajimin da mutumin ya dauka, in ji kafar labarai ta News Channel Nebraska.

Lee Meyer mazaunin garin Neligh—yana tuki tare da bajimi mai suna Howdy Doody, a kowace hanyar.

Hukumomin da suke kula da hanyoyi a yau da kullun kuma sun ga alama mai launin rawaya a gefen motar bayan sun duba sai ga bajimin a ciki.

“Jami’an sun samu kiran waya da ke nuna wata mota na shiga garin tare da saniya,” kamar yadda Kyaftin din ’Yan sanda Chad Reiman ya shaida wa tashar.

“Sun yi tunanin cewa zai zama dan maraki ne, ko wani karamin dabba ko wani abu da zai shiga cikin motar.

“Sakamakon haka, jami’in ya umarci jami’in da ke kula da hanyar ya dakatar da motar saboda dalilin tsaro,” in ji Reiman.

Reiman ya ci gaba da cewa, “Akwai wasu batutuwa masu muhimmanci game da wannan hali.

Jami’in ya zabi ya rubuta masa gargadi kuma ya roke shi ya dauki bajimin ya koma gida ya bar birnin.

“Ban san dalilin da ya sa yake yin hakan ba a ranar,” Reiman ya bayyana wa kafar labarai ta People.com

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai14 hours ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Ilimi16 hours ago

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu. Jakadan...

Labarai3 days ago

Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar...

Ilimi3 days ago

Daliban Jihar Kebbi Da Ke Kasashen Waje Za Su Sami Tallafin Naira Miliyan 309

Gwamnatin jihar Kebbi, ta amince da kashe sama da Naira miliyan Dari Uku da Tara, domin biyan tallafin karatu na...

Kasuwanci3 days ago

Kwari Masu Lalata Amfanin Gona Sun Mamaye Gonakin Tumatur A Kano

Shugaban kungiyar manoma ta jihar Kano, AFAN, Abdullahi Maibreadi, ya bukaci gwamnati a dukkan matakai da su taimaka wa manoma...

Fasaha3 days ago

Shugaba Tinubu Ya Kaddamar Shirin Bada Bashin Kayyaki Ga ‘Yan Kasa

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya ƙaddamar da kashin farko na tsarin karɓar bashin kaya ga ƴan ƙasar. Bayanin hakan na...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Jihar Kaduna Ta Rufe Bankin UBA Kan Kin Biyan Haraji

Hukumar Tara Kudaden Haraji ta Jihar Kaduna (KADIRS) ta raufe rassan bankin UBA kan kin biyan harajin Naira miliyan 14....

Labarai4 days ago

Mutum Biyar Sun Mutu Cikin Kwale-Kwalen ƴan Ci-Rani

Mutum biyar har da yaro sun mutu yayin da suke ƙoƙarin tsallake hanyar ruwa da ta ratsa Ingila da safiyar...

Kasuwanci4 days ago

CBN Ya Sake Karya Farashin Dala Zuwa N1,101

Babban Bankin Nigeria CBN ya sake sanar da matakin karya farashin dala daga N1,251 zuwa N1,101. CBN ya bayyana haka...

Ilimi4 days ago

Ƴan Sanda Za Su Yi Bincike Kan Makarantar Leads British

Rundunar ƴan sanda a babban birnin tarayya Abuja ta ce ta aika tawagar jami’anta zuwa makarantar Leads British bayan bidiyon...

Mafi Shahara