Connect with us

Labarai

Sheikh Daurawa Ya Amince Da Cigaba Da Jagorantar Hukumar Hisbah

Published

on

Kwamandan Hisbah ta jihar kano Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya dawo mukaminsa bayan sulhun da kungiyar Inuwar hadin kan malaman Kano ta jagoranta tsakanin sa da gwamnan jihar Abba Kabir Yusuf.

 

Idan za’a iya tunawa a ranar Juma’a ne Sheikh Daurawa ya bayyana Ajiye mukamin nasa bayan wasu kalamai da gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya yi, inda ya  Kalubalanci yadda hukumar take gudanar da wasu daga cikin aiyukan ta.

 

Da yake zantawa da Manema labarai Mai magana da yawun gwamnan jihar kano Sanusi Bature Dawakin Tofa yace an sami mahimtar junan ne a wani zama da  da aka yi tsakanin zauren malaman kano da Sheikh Daurawa da kuma gwamna Abba Kabir Yusuf.

Yace “dama tun da farko a wajen gwamnati Malam bai ajiye aikinsa ba, saboda bai rubuta ba , don haka Ina tabbatar da cewa an sami masalaha kuma malam zai cigaba da yin aikinsa yadda ya kamata.

A wani rubutaccen jawabi da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Sheikh  Aminu Ibrahim Daurawa ya tabbatar da yin sulhu a dare wannan rana ta Litinin.

Labarai

Labarai3 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai3 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai3 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi3 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai4 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai4 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai5 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai5 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai5 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara