Labarai
Sheikh Daurawa Ya Amince Da Cigaba Da Jagorantar Hukumar Hisbah
Kwamandan Hisbah ta jihar kano Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya dawo mukaminsa bayan sulhun da kungiyar Inuwar hadin kan malaman Kano ta jagoranta tsakanin sa da gwamnan jihar Abba Kabir Yusuf.
Idan za’a iya tunawa a ranar Juma’a ne Sheikh Daurawa ya bayyana Ajiye mukamin nasa bayan wasu kalamai da gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya yi, inda ya Kalubalanci yadda hukumar take gudanar da wasu daga cikin aiyukan ta.
Da yake zantawa da Manema labarai Mai magana da yawun gwamnan jihar kano Sanusi Bature Dawakin Tofa yace an sami mahimtar junan ne a wani zama da da aka yi tsakanin zauren malaman kano da Sheikh Daurawa da kuma gwamna Abba Kabir Yusuf.
Yace “dama tun da farko a wajen gwamnati Malam bai ajiye aikinsa ba, saboda bai rubuta ba , don haka Ina tabbatar da cewa an sami masalaha kuma malam zai cigaba da yin aikinsa yadda ya kamata.
A wani rubutaccen jawabi da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya tabbatar da yin sulhu a dare wannan rana ta Litinin.
-
Labarai4 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi5 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha5 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai5 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai5 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai5 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai3 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai5 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar