Connect with us

Labarai

EFCC Ta Cafke Manyan Motoci 21 Makare Da Kayan Abinci

Published

on

Hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, EFCC, ta cafke manyan motoci 21 makare da kayan abinci da sauran kayayyaki, wadanda za a tsallaka da su kasashen Chadi, da Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya da kuma jamhuriyar Kamaru.

A wata sanarwa da jami’in yada labarai da hulda da jama’a na hukumar, Dele Oyewale, ya fitar, ya ce jami’an hukumar shiyar Maiduguri sun cafke manyan motocin a wani samame da suka kai a manyan hanyoyin fita da ke kan titin Gamboru Ngala da Bama a jihar Borno.

Sanarwar ta bayyana cewa, da farko ba a gano kayan abincin ba saboda yadda aka boye su cikin dubara a cikin manyan motocin, sai da jami’an suka zurfafa bincike.

Ya kara da cewa, binciken da aka yi ya nuna cewa, an shirya manyan motocin ne zuwa  N’djamena, da Jamhuriyar Chadi, da Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya da kuma Kamaru, tare da lura da cewa, kamawar da aka yi za ta taimaka wajen dakile matsalar karancin abinci da masu fasa kwauri a fadin kasar ke haddasawa.

A cewar sanarwar, wadanda ake zargin a sun bayyana sunayensu kuma za a gurfanar da su a gaban kotu da zarar an kammala bincike.

Daga Dauda Iliya

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai11 hours ago

Ma’aikatan Ceto Na Cigaba Da Neman Jirgin Shugaban Kasar Iran Da Ya Bace

Da yammacin yau lahadi ne tarin ma’aikatan ceto suka bazama wajen aiki gano jirgi mai saukar ungulu dauke da shugaba...

Labarai4 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai4 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai4 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi4 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai5 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai5 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai6 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai6 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai6 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Mafi Shahara