Labarai
EFCC Ta Cafke Manyan Motoci 21 Makare Da Kayan Abinci
Hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, EFCC, ta cafke manyan motoci 21 makare da kayan abinci da sauran kayayyaki, wadanda za a tsallaka da su kasashen Chadi, da Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya da kuma jamhuriyar Kamaru.
A wata sanarwa da jami’in yada labarai da hulda da jama’a na hukumar, Dele Oyewale, ya fitar, ya ce jami’an hukumar shiyar Maiduguri sun cafke manyan motocin a wani samame da suka kai a manyan hanyoyin fita da ke kan titin Gamboru Ngala da Bama a jihar Borno.
Sanarwar ta bayyana cewa, da farko ba a gano kayan abincin ba saboda yadda aka boye su cikin dubara a cikin manyan motocin, sai da jami’an suka zurfafa bincike.
Ya kara da cewa, binciken da aka yi ya nuna cewa, an shirya manyan motocin ne zuwa N’djamena, da Jamhuriyar Chadi, da Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya da kuma Kamaru, tare da lura da cewa, kamawar da aka yi za ta taimaka wajen dakile matsalar karancin abinci da masu fasa kwauri a fadin kasar ke haddasawa.
A cewar sanarwar, wadanda ake zargin a sun bayyana sunayensu kuma za a gurfanar da su a gaban kotu da zarar an kammala bincike.
Daga Dauda Iliya
-
Labarai5 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha6 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai6 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai4 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai6 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar
-
Labarai6 days ago
Varane zai bar Manchester United