Connect with us

Kasuwanci

EFCC Ta Tsare ’Yan Canji A Kasuwar WAPA

Published

on

Hukumar EFCC ta tsare wasu ’yan kasuwa a samamen da jami’anta suka kai kasuwar ’yan canji ta WAPA da ke Jihar Kano ranar Laraba.

A safiyar Laraba jami’an hukumar cikin shigar burtu, suka yi dirar mikiya a kasuwar ta WAPA a wani yunkuri na yaki da ayyukan masu boye Dala.

Wani ganau mai suna Malam Isma’ila Zico, ya ce jami’an na EFCC “Sun nuna kwarewa, sai daga bisani muka gano cewa tun safe suke nan.

“Lokacin da za su fara aikin ne sai muka ga masu jaket dinsu sun shigo, suka yi wa wajen yan canji kawanya.

“Ban san ko mutum nawa suka kama ba, amma dai sun tafi da wasu ’yan canjin,” in ji Zico, wanda ya ce an kai samemen ne a yayin da ake tsaka da hadahadar kasuwanci.

EFCC ta kai samemen ne a yayin da ake tsaka da hadahadar kasuwanci, suka yi awon gaba da wasu daga cikin yan kasuwar.

Shugaban ’yan canji na kasuwar, Alhaji Sani Salisu Dada, ya tabbatar kamen na ranar Laraba, wanda ya ce za a binciki wadanda aka yi awon gaban da su na.

A ceawrsa, jami’an EFCC sun kai samamen ne domin shawo kan matsalar masu boye dala da kuma ’yan canji masara lasisi.

Amma ya kara da cewa an ci gaba da harkoki yadda aka saba a kasuwar, kuma a shirye suke su ba da hadin kai ga hukuma.

Hakan na zuwa ne sakamakon ci gaba da tashin gwauron zabo da dalar ke yi a wurin ’yan canji a sassan kasar, inda farashin dalar ya kai N1,900.

A ranar talata gwamnatin tarayya ta umarci hukumomin tsaro da su dauki matakin kamawa, bincike da kuma hukunta masu wannan dabi’a.

Ko a ranar talata jami’an EFCC sun kai makamancin wannan samame a kasuwar ‘yan canji da ke unguwar Zone 4 da ke Abuja.

A safiyar Laraba ma rahotanni sun nuna cewa an kai irin wannan samame a kasuwar ’yan canji da ke Unguwar Sabo a garin Ibadan, Jihar Oyo.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai13 hours ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai14 hours ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai15 hours ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi16 hours ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai1 day ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai2 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai3 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai3 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai3 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara