Connect with us

Labaran Gida

An Bai Wa Kowanne Gwamna N30bn Ya Rage Tsadar Rayuwa A Jiharsa — Majalisar Dattawa

Published

on

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya ce Gwamnatin Tarayya ta bai wa kowanne gwamnan jiha naira biliyan 30 domin rage wa talakawa raɗaɗin tsadar rayuwar da suke fuskanta.

Akpabio ya bayyana haka ne a yayin zaman majalisar na ranar Talata, a ci gaba da tattauna irin halin ƙuncin da jama’ar kasar suka samu kansu a ciki, wanda ake dangantawa da cire tallafin mai.

Shugaban majalisar ya ce ya samu wadannan bayanai ne daga wajen Hukumar Tara Kuɗaɗen Haraji ta Kasa wadda ta miƙa wa jihohin waɗannan kuɗaɗen da ake magana a kansu.

Akpabio ya ce waɗannan kuɗaɗen daban ne da naira biliyan bib-biyu da aka bai wa gwamnonin a watan Satumbar bara daga cikin biliyan biyar-biyar na rancen samar wa jama’ar su tallafin rage raɗaɗin cire tallafin man fetur.

Shugaban majalisar ya bai wa gwamnonin shawara wajen yin amfani da waɗannan makudan kuɗaɗe ta hanyar da ta dace domin ganin jama’ar jihohin su sun samu tallafin da ya dace, musamman a bangaren abin da ya shafi abinci.

Akpabio ya ce ana iya cimma nasarar gabatar da tallafin ne ta hanyar amfani da shugabannin kananan hukumomi saboda kusancin su da mutanen da ke yankunan karkara.

Shugaban majalisar wanda ya yi Allah wadai da zanga-zangar da aka gani a wasu jihohin kasar da ake danganta su da tsadar rayuwa, ya zargi ‘yan adawa da daukar nauyin su, duk da kokarin da ya ce Majalisar Dattawan na yi domin tunkarar matsalar tare da Gwamnatin Tarayya.

Akpabio ya ce babu wani mahaifin da ke fatar ganin ɗansa ya kwanta ba tare da ya ci abinci ba, saboda haka ya buƙaci takwarorinsa da su mayar da hankali a kan ɗaukar matakin samo abinci duk inda yake domin wadata jama’a.

Labarai

Labarai7 hours ago

Ma’aikatan Ceto Na Cigaba Da Neman Jirgin Shugaban Kasar Iran Da Ya Bace

Da yammacin yau lahadi ne tarin ma’aikatan ceto suka bazama wajen aiki gano jirgi mai saukar ungulu dauke da shugaba...

Labarai4 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai4 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai4 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi4 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai5 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai5 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai6 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai6 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai6 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Mafi Shahara