Connect with us

Labarai

Ba Gudu Ba Ja Da Baya Kan Zanga-Zangar Gama-Gari Da Za Mu Gudanar — NLC

Published

on

Kungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC) ta sanar da cewa babu gudu babu ja da baya dangane da zanga-zangar gama-gari da za ta gudanar a ranar 27 da 28 ga wannan wata na Fabarairu.

Sanarwar dai martani ce ga Hukumar Tsaron Farin Kaya (DSS)da ta bukaci kungiyar kwadagon ta sauya tunani kan zanga-zangar da a cewarta babu lallai ta wanye lafiya ba.

a safiyar wannan Larabar ce DSS ta yi kira ga kungiyar kwadagon da ta jingine shirinta na gudanar da zanga-zanga domin ci gaba da wanzuwar zaman lafiya da walwalar jama’a.

Gargadin DSS na zuwa ne tun bayan da a Juma’ar da ta gabata, NLC ta ayyana zanga-zangar kwanaki 2 a fadin kasar nan kan halin matsin da ‘yan Najeriya ke fuskanta da kuma matsalar tabarbarewar harkokin tsaro a fadin kasar.

Sanarwar ta kara da cewar gwamnatoci a dukkanin matakai na iya bakin kokarinsu wajen rage radadin halin kuncin da ake ciki, don haka ya kamata a kyautata musu zato.

Sai dai da ya ke martani kan wannan gargadi na DSS, Shugaban NLC Joe Ajaero, ya ce maimakon yi wa kungiyarsu barazana, kamata ya yi DSS ta daura damarar kama duk wadanda za su kawo hargitsi a yayin zanga-zangar.

A cewar Kwamared Ajaero, tarihi ba zai taba yafe wa ƙungiyar ƙwadago ba ma damar ta zauna ta yi shiru kuma ta nade hannu alhali ’yan Najeriya na ci gaba da fuskantar tsadar rayuwa ba.

Shugaban kungiyar kwadagon, wanda ya bayyana matakin da ke tafe a matsayin “zanga-zangar lumana kan tsadar rayuwa da ba za a lamunta ba,” ya kara da cewa kungiyar kwadagon ba za ta nade hannunta ba yayin da ‘yan Najeriya ke ci gaba da rayuwa cikin kunci.

“Muna so DSS ta sani cewa babu inda aka taba samun tashin hankula a zanga-zagar lumana da kungiyar kwadago ta taba gudanarwa, don haka batun mu janye wannan bai taso ba.”

Shugaban NLC ya koka kan yadda tattalin arzikin kasar ya tabarbare yana mai cewa yanzu haka darajar naira ta kara kundunbala inda farashinta a kasuwar canjin kudi ya kai N1,900 kan kowacce dalar Amurka daya.

Ya ba da tabbacin cewa babu wanda ya ke son ci gaban Najeriya kamar kungiyar kwadago kuma ba za ta taba yin wani abu da zai jawo rashin zaman lafiya ba.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai9 hours ago

Ma’aikatan Ceto Na Cigaba Da Neman Jirgin Shugaban Kasar Iran Da Ya Bace

Da yammacin yau lahadi ne tarin ma’aikatan ceto suka bazama wajen aiki gano jirgi mai saukar ungulu dauke da shugaba...

Labarai4 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai4 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai4 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi4 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai5 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai5 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai6 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai6 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai6 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Mafi Shahara