Connect with us

Labarai

An Gina Riyojin Burtsatse ga yankunan da aka kai hari a Jihar Plateau

Published

on

Asusun tallafaws wadanda wata masifa ta fadawa ya gina riyojin burtsatse ga wasu al’ummomi da rikicin baya bayan nan ya Shafa a jihar Plateau.

Mai bada shawara na musamman ga shugaban asusun Janar Theophilus Danjuma, Mrs Toyosi Akenrele-Ogunsiji tace asusun na da manufar yaye wahalhalun da ‘yan Nijeriya suke sha.

Wakilinmu Josiah Buzun na dauke da karin bayani daga Jos.

Hare haren da aka rika kaiwa wasu kananan hukumomin jihar Plateau yayi sanadiyar jama’a da dama suka rasa kayyakin more rayuwarsu.

Wannan ne dalilin da ya sa asusun tallafawa wadanda masifa ta Shafa karlashin jagorancin Janar Theophilus Danjuma ya tona riyojin burtsatse don samarda ruwan sha ga al’umma.

An gina wadannan riyojin masu aiki da hasken Rana ga al’ummomin Doruwa, Babuje da Gassa a karamar hukumar Barikin Ladi, Sai Kuma a Ariri dake karamar hukumar Bassa da Kuma al’ummomin Sop dake tsalleken dogo a karamar hukunar Riyom.

Mrs. Akenrele Ogunsiji da ta wakilci shugabar asusun wajen bude wadannan ayukkan, tace mutane na bukatar tsaftaccen ruwan sha da wasu kayyayakin more rayuwa, don haka suke fara raba hatsi da Kuma kayan koyarwa da Kuma tallafawa don karfafa jama’a su dogara da kansu.

Mrs. Akenrele Ogunsiji tayi bayanin cewa, duk Wanda ke musu aiki da ya kasa gabatar da shi yanda ya dace zasu hukunta shi.

Shi kuma babbar daraktan asusun Farfesa Nana Tanko tace wajibi kowa ya amfana da wadannan riyojin da aka tona.

A jawabinsa babban sakataren hukumar bada agajin gaggauwa na jihar Plateau Mr. Sunday Abubu ya hori wadanda suka amfana da wannan aikin su kula da shi sosai.

Shugaban al’ummar Gassa da ke karamar hukunar Barikin Ladi James Toma ya godewa wannan asusun da shugabansa Janar Theophilus Danjuma saboda sanya farin cikin a tsakanin talakawan kasan Nan.

Wadanda suka amfana da shirin bayan yabon wannan asusun sun kuma bayyana imanin cewa wannan aikin zai taimaka wajen samar da ruwansha mai tsafta tare da kawarda cutuka da ake samu daga ruwa tare da fatan za a Sami Karin irin wannan aikin.

Josiah/Shafii Wababe

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai10 hours ago

Ma’aikatan Ceto Na Cigaba Da Neman Jirgin Shugaban Kasar Iran Da Ya Bace

Da yammacin yau lahadi ne tarin ma’aikatan ceto suka bazama wajen aiki gano jirgi mai saukar ungulu dauke da shugaba...

Labarai4 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai4 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai4 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi4 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai5 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai5 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai6 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai6 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai6 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Mafi Shahara