Labarai
An Gina Riyojin Burtsatse ga yankunan da aka kai hari a Jihar Plateau
Asusun tallafaws wadanda wata masifa ta fadawa ya gina riyojin burtsatse ga wasu al’ummomi da rikicin baya bayan nan ya Shafa a jihar Plateau.
Mai bada shawara na musamman ga shugaban asusun Janar Theophilus Danjuma, Mrs Toyosi Akenrele-Ogunsiji tace asusun na da manufar yaye wahalhalun da ‘yan Nijeriya suke sha.
Wakilinmu Josiah Buzun na dauke da karin bayani daga Jos.
Hare haren da aka rika kaiwa wasu kananan hukumomin jihar Plateau yayi sanadiyar jama’a da dama suka rasa kayyakin more rayuwarsu.
Wannan ne dalilin da ya sa asusun tallafawa wadanda masifa ta Shafa karlashin jagorancin Janar Theophilus Danjuma ya tona riyojin burtsatse don samarda ruwan sha ga al’umma.
An gina wadannan riyojin masu aiki da hasken Rana ga al’ummomin Doruwa, Babuje da Gassa a karamar hukumar Barikin Ladi, Sai Kuma a Ariri dake karamar hukumar Bassa da Kuma al’ummomin Sop dake tsalleken dogo a karamar hukunar Riyom.
Mrs. Akenrele Ogunsiji da ta wakilci shugabar asusun wajen bude wadannan ayukkan, tace mutane na bukatar tsaftaccen ruwan sha da wasu kayyayakin more rayuwa, don haka suke fara raba hatsi da Kuma kayan koyarwa da Kuma tallafawa don karfafa jama’a su dogara da kansu.
Mrs. Akenrele Ogunsiji tayi bayanin cewa, duk Wanda ke musu aiki da ya kasa gabatar da shi yanda ya dace zasu hukunta shi.
Shi kuma babbar daraktan asusun Farfesa Nana Tanko tace wajibi kowa ya amfana da wadannan riyojin da aka tona.
A jawabinsa babban sakataren hukumar bada agajin gaggauwa na jihar Plateau Mr. Sunday Abubu ya hori wadanda suka amfana da wannan aikin su kula da shi sosai.
Shugaban al’ummar Gassa da ke karamar hukunar Barikin Ladi James Toma ya godewa wannan asusun da shugabansa Janar Theophilus Danjuma saboda sanya farin cikin a tsakanin talakawan kasan Nan.
Wadanda suka amfana da shirin bayan yabon wannan asusun sun kuma bayyana imanin cewa wannan aikin zai taimaka wajen samar da ruwansha mai tsafta tare da kawarda cutuka da ake samu daga ruwa tare da fatan za a Sami Karin irin wannan aikin.
Josiah/Shafii Wababe
-
Labarai5 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha6 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai6 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai4 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai6 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar
-
Labarai6 days ago
Varane zai bar Manchester United