Labarai
Sojoji Sun Ceto Mutane 15 Da Aka Sace A Zamfara
Dakarun soji sun hallaka wani dan bindiga kuma sun ceto mutane 15 da aka yi garkuwa da su a Jihar Zamfara.
Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da kakakin rundunar Operation Hadarin Daji, Laftanar Sulaiman Omale ya fitar a Gusau ranar Talata.
Kamfanin Dillacin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito Laftanar Sulaiman na cewa, “Mun samu kiran gaggawa cewa ’yan bindiga sun kai hari yankin Tsohuwar Tasha da ke Karamar Hukumar Kauran Namoda a Jihar Zamfara, shi ne dakarunmu suka kai dauki.
“A ranar 5 ga Maris, 2024, sojojin sun yi mummunar artabu da ’yan bindigar, wanda hakan ya tilastawa ’yan bindigar tserewa, wasu suka fada ruwa.
A cewarsa, wadanda aka yi garkuwa da su sun hada da mata takwas da maza bakwai.
“A yanzu dai zan iya cewa zaman lafiya ya samu a yankin, kuma mutane sun samu kwarin gwiwa, ganin yadda dakarunmu ke ci gaba da sintiri”.
Babban kwamandan sojin runduna ta 8, da ke Sakkwato, Manjo-Janar Godwin Mutkut, ya yaba da kwazo da kuma jajircewar sojojin.
-
Labarai5 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha6 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai6 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai4 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai6 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar
-
Labarai6 days ago
Varane zai bar Manchester United