Labarai
Yadda Aka Kashe Jagoran ’Yan Ta’addan Katsina Da Yaransa
Sojojin Najeriya sun yi nasarar kashe Maikusa, wani kasurgumin dan ta’adda da ke jagorantar hare-hare a Jihar Katsina.
Maikusa ne mataimakin wani fitaccen dan ta’addan da ya addabi jama’ar Jihar Katsina Modi Modi, wanda ake nema ruwa a jallo.
Daraktan hulda da jama’a na rundunar sojin Najeriya, Manjo-Janar, Onyema Nwachukwu ne ya sanar cewa sojojin sun hallaka Maikusa da wasu ’yan ta’adda uku ne a ranar Litinin, a tsakanin kananan hukumomin Kurfi da Safana da ke jihar bayan bata kashin da sojin suka yi da ’yan ta’addan.
Ya ce, wannan gagarumin aiki ya yi nasarar kawar da ’yan ta’addar da suka jima suna addabar al’ummar yankunan.
Ministan Tsaron Najeriya, Muhammad Badaru Abubakar, ya ce sojoji a cikin ’yan watannin da suka gabata sun kashe akalla manyan jagororin ’yan tada kayar baya bakwai a kasar.
Ministan ya bayyana haka ne a wata hira da manema labarai a Jaji ranar Talata.
Ministan wanda ya kai ziyarar aiki, ya gabatar da jawabi ga sojojin da ke halartar wani taron kara wa juna sani da kwalejin yaki da ta’addanci da ’yan ta’adda.
-
Labarai5 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha6 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai6 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai4 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai6 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar
-
Labarai6 days ago
Varane zai bar Manchester United